< Acts 23 >
1 And Paul, after looking intently at the council, said, Men, brothers, I have been a citizen in all good conscience to God until this day.
Bulus ya zuba wa Majalisar ido ya ce, “’Yan’uwana, na cika aikina ga Allah cikin lamiri mai kyau har yă zuwa yau.”
2 And the high priest Ananias ordered those who stood by him to strike his mouth.
Da jin wannan Ananiyas babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.
3 Then Paul said to him, God is going to smite thee, a whitewashed wall. Thou even sit judging me according to the law, and violating law, thou command me to be struck?
Sai Bulus ya ce masa, “Allah zai buge ka, kai farin bango! Ka zauna a can kana hukunta ni bisa ga doka, ga shi kai kanka kana ƙetare dokar ta wurin ba da umarni a buge ni!”
4 And those who stood by said, Thou revile God's high priest?
Waɗanda suke tsaye kusa da Bulus kuwa suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”
5 And Paul said, I had not known, brothers, that he is a high priest, for it is written, Thou shall not speak ill of a ruler of thy people.
Bulus ya amsa ya ce, “’Yan’uwa, ai, ban san cewa shi ne babban firist ba; gama yana a rubuce cewa, ‘Kada ka yi mugun magana game da mai mulkin mutanenka.’”
6 But when Paul ascertained that the one part were Sadducees and the other Pharisees, he cried out in the council, Men, brothers, I am a Pharisee, son of a Pharisee. About the hope and resurrection of the dead I am judged.
Bulus, da ya gane cewa waɗansu daga cikinsu Sadukiyawa ne sauran kuma Farisiyawa ne, sai ya ɗaga murya a Majalisar ya ce, “’Yan’uwana, ni Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ana mini shari’a saboda begen da nake da shi a kan tashin matattu.”
7 And when he said this, there developed a conflict of the Pharisees and Sadducees, and the group was divided.
Da ya faɗi haka, sai gardama ta tashi tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, taron kuwa ya rabu biyu.
8 For in fact Sadducees say to be no resurrection nor agent nor spirit, but Pharisees acknowledge them all.
(Sadukiyawa suna cewa babu tashin matattu, babu mala’iku ko ruhohi. Amma Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.)
9 And there developed a great clamor. And some of the scholars of the Pharisees part having risen, they argued vehemently, saying, We find nothing wrong in this man. But if a spirit spoke to him, or an agent, we should not fight against God.
Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
10 And a great conflict having developed, the chief captain, having been alarmed lest Paul might be torn apart by them, commanded the soldiers to go down and take him away from the midst of them, and bring him into the fort.
Gardamar kuwa ta yi tsanani har shugaban ƙungiyar sojan ya ji tsoro za su yayyage Bulus. Ya umarci sojoji su tafi su ƙwace shi ƙarfi da yaji daga wurinsu su kawo shi cikin barikin soja.
11 And the following night the Lord, having stood by him, said, Cheer up, Paul, for as thou have testified these things about me at Jerusalem, so thou must testify also at Rome.
Kashegari da dare Ubangiji ya tsaya kusa da Bulus ya ce, “Ka yi ƙarfin hali! Don kamar yadda ka yi shaida game da ni a Urushalima, haka kuma lalle, za ka yi shaidata a Roma.”
12 And when it became day, some of the Jews, having made a conspiracy, put themselves under a curse, saying neither to eat nor to drink until they would kill Paul.
Kashegari, Yahudawa suka ƙulla makirci suka kuma yi rantsuwa cewa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe Bulus.
13 And there were more than forty who made this conspiracy,
Fiye da mutane arba’in ne suka ƙulla wannan makirci.
14 who, having come near to the chief priests and the elders, said, We have put ourselves under a curse, a curse to taste of nothing until we would kill Paul.
Suka je wajen manyan firistoci da dattawa suka ce, “Mun yi babbar rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba sai mun kashe Bulus.
15 Now therefore ye with the council report to the chief captain that tomorrow he may bring him down to you, as though going to inquire more accurately the things about him. And we, before he comes near, are prepared to kill him.
Saboda haka, sai ku da Majalisa sai ku roƙi shugaban ƙungiyar sojan yă kawo shi a gabanku kamar kuna so ku ƙara samun cikakken bayani game da zancensa. Mu kuwa muna a shirye mu kashe shi kafin yă iso nan.”
16 But the son of Paul's sister, having heard of the ambush, having come and entered into the fort, he informed Paul.
Amma da ɗan’yar’uwar Bulus ya ji wannan makirci, sai ya tafi cikin barikin soja ya gaya wa Bulus.
17 And Paul, having called one of the centurions, said, Take this young man to the chief captain, for he has something to inform him.
Sai Bulus ya kira ɗaya daga cikin jarumawan ya ce, “Ka kai wannan saurayi wurin shugaban ƙungiyar soja; yana da wani abin da zai faɗa masa.”
18 Indeed therefore having taken him, he brought him to the chief captain, and says, Paul the prisoner, having called me, asked me to bring this young man to thee, who has something to say to thee.
Saboda haka ya ɗauke shi ya kai wajen shugaban ƙungiyar sojan. Jarumin ya ce, “Bulus, ɗan kurkukun nan ya kira ni, ya roƙe ni in kawo wannan saurayi a wurinka domin yana da wani abin da zai faɗa maka.”
19 And the chief captain having grasped his hand, and having gone in private, he asked him, What is it that thou have to inform me?
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya kama hannun saurayin ya ja shi gefe, ya tambaye shi cewa, “Mene ne kake so ka gaya mini?”
20 And he said, The Jews have agreed to ask thee that tomorrow thou would bring Paul down to the council, as though going to inquire something more accurately about him.
Saurayin ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kawo Bulus a gaban Majalisa gobe kamar suna neman ƙarin cikakken bayani game da Bulus.
21 Therefore thou should not be persuaded by them, for more than forty men of them wait to ambush him, who have put themselves under an oath, neither to eat nor drink until they have killed him. And now they are ready, expecting the promise from thee.
Kada ka yarda da su, domin fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa. Sun yi rantsuwa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe shi. Suna nan a shirye yanzu, suna jira ka amince da roƙonsu.”
22 Indeed therefore the chief captain dismissed the young man, having ordered, Tell no man that thou have shown these things to me.
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya sallami saurayin ya kwaɓe shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka faɗa mini wannan.”
23 And having summoned a certain two of the centurions, he said, Prepare two hundred soldiers that they may go to Caesarea, and seventy horsemen, and two hundred spearmen at the third hour of the night.
Sai ya kira biyu daga cikin jarumawansa, ya umarce su cewa, “Ku shirya sojoji ɗari biyu, da masu hawan dawakai saba’in da kuma masu māsu ɗari biyu su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.
24 And provide beasts, so that after mounting Paul, they may bring him safely to Felix the governor,
Ku shirya wa Bulus dawakai da zai hau don a kai shi wurin Gwamna Felis lafiya.”
25 after writing a letter containing this form:
Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka,
26 Claudius Lysias to the eminent governor Felix, greeting.
Kalaudiyus Lisiyas. Zuwa ga Mai Girma, Gwamna Felis. Gaisuwa.
27 This man who was seized by the Jews, and was going to be killed by them, having stood by with the soldiers, I rescued him, having learned that he is a Roman.
Yahudawa sun kama wannan mutum suna kuma dab da kashe shi, amma na zo da sojojina na ƙwato shi, saboda na ji shi ɗan ƙasar Roma ne.
28 And wanting to know for what reason they accused him, I brought him down to their council,
Na so in san abin da ya sa suke zarginsa, saboda haka na kawo shi a gaban Majalisarsu.
29 whom I found accusing about issues of their law, having not one accusation worthy of death or of bonds.
Na tarar cewa zargin da ake masa ya shafi waɗansu abubuwan da suka shafi dokarsu ne, amma ba wani zargi a kansa da ya isa kisa ko a daure shi.
30 And when it was reported to me of a plot going to be against the man by the Jews, I immediately sent him to thee, also having commanded the accusers to speak before thee the things against him. Be strong.
Sa’ad da na sami labari cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, sai na aika shi wurinka nan da nan. Na kuma umarci masu zarginsa su kai ƙararsu gare ka.
31 Indeed therefore, the soldiers, according to that which was precisely arranged for them, having taken Paul, they brought him through the night to Antipatris.
Saboda haka sojojin, don cika umarni, suka ɗauki Bulus da dad dare suka kawo shi har Antifatiris.
32 But on the morrow they returned to the fort, having allowed the horsemen to depart with him,
Kashegari suka bar masu hawan dawakai suka ci gaba da shi, yayinda sojojin suka koma barikin soja.
33 who, after coming to Caesarea and having delivered the letter to the governor, also presented Paul to him.
Sa’ad da masu hawan dawakai suka isa Kaisariya, sai suka ba wa gwamna wasiƙar suka kuma miƙa masa Bulus.
34 And the governor having read it, and having questioned from what province he was, and having found out that he was from Cilicia,
Gwamna ya karanta wasiƙar ya kuma tambaya ko daga wanda lardi ne ya fito. Da ya ji cewa shi daga Silisiya ne,
35 he said, I will hear thee when thine accusers also will arrive. And he commanded him to be kept in the Praetorium of Herod.
sai ya ce, “Zan ji batunka lokacin da masu zarginka suka iso.” Sa’an nan ya ba da umarni a kai Bulus a tsare shi a fadar Hiridus.