< Acts 2 >

1 And while fulfilling the day of Pentecost, they were all together at the same place.
Da ranar Fentikos ta zo, dukansu suna tare wuri daya.
2 And suddenly there developed a sound from the sky as of a forceful wind moving, and it filled the entire house where they were sitting.
Nan da nan sai ga wata kara daga sama kamar ta babbar iska, kuma ta sauko ta cika duka gidan inda suke zaune.
3 And there appeared to them dividing tongues, as of fire, and they settled upon each one of them.
Sai ga wasu harsuna kamar na wuta sun bayyana a garesu aka rarraba su, kuma suka zauna bisa kowannensu.
4 And they were all filled of the Holy Spirit, and began to speak with other tongues, as the Spirit gave them to declare.
Dukansu suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka fara magana da wadansu harsuna, yadda Ruhu ya ba su iko su yi magana.
5 Now there were dwelling at Jerusalem, Jews, devout men from every nation under heaven.
A lokacin akwai Yahudawa dake zaune a Urushalima, mutanen Allah, daga kowace kasa karkashin sama.
6 And the sound of this that happened brought the multitude together. And it was bewildered because each one heard them speaking in his own language.
Da suka ji wannan kara jama'a duk suka taru suka rude saboda kowannensu ya ji suna magana da harshensa.
7 And they were amazed and marveled, saying to each other, Behold, are not all these men who speak Galileans?
Suka yi mamaki matuka; suka ce, ''Lallai, wadannan duka ba Galiliyawa ba ne?
8 And how do we each hear our own language in which we were born?
Yaya mu ke jinsu duka, kowannensu na magana a cikin harshen da aka haife mu?
9 Parthians and Medes and Elamites, and those dwelling in Mesopotamia, and Judea and Cappadocia, Pontus and Asia,
Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya,
10 and Phrygia and Pamphylia, Egypt and the parts of Libya along Cyrene, and those Roman aliens, including Jews and proselytes,
cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma,
11 Cretes and Arabians. We hear them speaking in our tongues the great things of God.
Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah.''
12 And they were all amazed, and were perplexed, others saying to others, Whatever does this intend to be?
Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, ''Menene ma'anar wannan?''
13 But others, mocking said, They are filled of wine.
Amma wasu suka yi ba'a suka ce, ''Sun bugu ne da sabon ruwan inabi.''
14 But Peter having stood up with the eleven, raised his voice and spoke out to them, saying, Jewish men, and all who dwell at Jerusalem, be this known to you, and listen to my sayings.
Amma Bitrus ya tashi tare da sha dayan, ya daga murya ya ce da su, ''Mutanen Yahuda da dukanku dake zaune a Urushalima, bari ku san wannan; ku saurari maganata.
15 For these men are not drunken, as ye suppose, for it is the third hour of the day.
Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.
16 But this is that which was spoken through the prophet Joel:
Amma wannan shine abinda aka fada ta wurin annabi Yowel.
17 And it will be in the last days, says God, I will pour out from my Spirit upon all flesh. And your sons and your daughters will prophesy, and your young men will see visions, and your elders will dream dreams.
Allah ya ce, 'Haka zai kasance a kwanakin karshe, zan zubo Ruhuna a kan dukan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci, kuma samarinku za su ga wahayoyi, kuma tsofaffinku za su yi mafarkai.
18 And also on my bondmen and on my bondmaids in those days I will pour out from my Spirit, and they will prophesy.
Haka kuma a bisa bayi na maza da mata, a kwanakin nan zan zubo da Ruhuna, kuma za su yi anabci.
19 And I will give wonders in the heaven above, and signs on the earth beneath, blood, and fire, and vapor of smoke.
Zan nuna al'ajibai a sararin sama da kuma alamu a bisa duniya, jini da wuta, da girgije.
20 The sun will be changed into darkness, and the moon into blood, before that great and wonderful day of the Lord comes.
Rana zata juya ta koma duhu kuma wata ya koma jini, kafin Babbar ranan nan ta Ubangiji ta zo.
21 And it will be, that every man, whoever may call on the name of the Lord will be saved.
Zai kuma zama dukan wanda ya kira ga sunan Ubangiji zai sami ceto.
22 Men, Israelites, hear ye these words. Jesus the Nazarene, a man shown by God among you by miracles and wonders and signs, which God did by him in the midst of you, as ye yourselves also know,
Mutanen Isra'ila, ku saurari wadannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar da shi gareku ta wurin manyan ayyuka da ban mamaki da alamu da Allah ya yi ta wurinsa a tsakiyarku, kamar yadda ku da kanku kuka sani.
23 this man, having been designated (by the purpose and foreknowledge of God) a man delivered up, ye, having taken by lawless hands, killed, having crucified,
Saboda tabbataccen shiri da riga sani na Allah, aka bayar dashi, ku kuma, ta hannun mutane 'yan tawaye, kuka gicciye shi kuma kuka kashe shi.
24 whom God raised up, having loosed the pangs of death, because it was not possible for him to be held by it.
Wanda Allah ya tayar, bayan ya cire zafin mutuwa daga gareshi, saboda ba zai yiwu ba ta rike shi.
25 For David speaks for him: I beheld the Lord always before me, because he is at my right hand, so that I may not be moved.
Gama, game da shi, 'Ina ganin Ubangiji a gabana ko yaushe, domin yana gefen hannun damana saboda kada in firgita.
26 Because of this my heart rejoiced, and my tongue was glad. And moreover my flesh will also rest in hope.
Saboda haka zuciyata na farin ciki harshena yana yin murna. Kuma, jikina zai zauna gabagadi.
27 Because thou will not leave my soul in Hades, nor will thou give thy Holy man to see decay. (Hadēs g86)
Gama ba za ka watsar da raina a lahira ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka ya ga ruba ba. (Hadēs g86)
28 Thou made known to me the paths of life. Thou will fill me of joy with thy countenance.
Ka bayyana mani hanyar rai; da fuskarka zaka cika ni da farin ciki.
29 Men, brothers, being permitted to speak to you with openness about the patriarch David, that he both perished and was buried, and his sepulcher is with us to this day.
'Yan'uwa, zan yi magana da ku gabagadi game da baba Dauda: ya mutu kuma aka bizne shi, kuma kabarinsa na nan tare da mu har yau.
30 Being therefore a prophet, and knowing that God had sworn with an oath to him, to raise the Christ from the fruit of his loins according to flesh to sit upon his throne.
Domin haka, don shi annabi ne kuma ya san Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa daga cikin zuriyarsa zai sanya wani bisa kursiyinsa.
31 Having foreseen this, he spoke about the resurrection of the Christ, that his soul was not left behind in Hades, nor did his flesh see decay. (Hadēs g86)
Ya hango wannan al'amari kuma ya yi magana game da tashin Almasihu, 'Ba ayi watsi da shi ba a lahira, kuma jikinsa bai ga rubewa ba.' (Hadēs g86)
32 This Jesus, God raised up, of which we are all witnesses.
Wannan Yesun - Allah ya tashe shi, wanda dukanmu shaidu ne.
33 Therefore, exalted by the right hand of God, and having received the promise of the Holy Spirit from the Father, he poured out this that ye now see and hear.
Saboda haka yadda aka tashe shi zuwa hannun dama na Allah kuma ya karbi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, shine ya zubo mana wannan da kuke gani kuma kuke ji.
34 For David did not ascend into the heavens, but he himself says, The Lord said to my Lord, Sit thou at my right hand
Dauda bai hau zuwa sama ba, amma ya ce, ''Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna hannun dama na,
35 until I place thine enemies a footstool of thy feet.
har sai na maida makiyanka abin takawar sawunka.'''
36 Therefore let all the house of Israel know assuredly, that God has made him, this Jesus whom ye crucified, both Lord and Christ.
Saboda haka, bari gidan Isra'ila su sani tabbas wannan Yesun wanda kuka gicciye, Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu.
37 Now having heard this, they were pierced in the heart, and said to Peter and the other apostles, Men, brothers, what will we do?
Da suka ji haka sai suka soku a zukatansu, suka cewa Bitrus da sauran manzanni, '''Yan'uwa me za mu yi?''
38 And Peter said to them, Repent ye, and be immersed each of you in the name of Jesus Christ for the remission of sins, and ye will receive the gift of the Holy Spirit.
Sai Bitrus ya ce masu, ''Ku tuba ayi wa kowannenku baftisma, cikin sunan Yesu Almasihu domin gafarar zunubanku, kuma za ku karbi baiwar Ruhu Mai Tsarki.
39 For the promise is to you, and to your children, and to all those in afar, as many as the Lord our God may call.
Domin alkawarin a gareku ne da 'ya'yanku da duk wadanda ke nesa, dukan iyakar mutanen da Ubangiji Allahnmu zai kira.''
40 And with many more other words he testified and exhorted them, saying, Be saved from this crooked generation.
Da maganganu da yawa ya ba da shaida kuma ya karfafa su; ya ce, ''Ku ceci kan ku daga wannan muguwar tsara.''
41 Indeed therefore those who received his word gladly, were immersed. And there were added in that day about three thousand souls.
Sai suka karbi maganar sa kuma aka yi ma su baftisma, a wannan rana kuma aka sami karin rayuka wajen dubu uku.
42 And they were continuing steadfastly in the apostles doctrine, and in fellowship, and in the breaking of bread, and the prayers.
Su ka cigaba cikin koyarwar manzanni da zumunta, cikin kakkaryawar gurasa da kuma cikin addu'o'i.
43 And fear developed in every soul. And many wonders and signs occurred through the apostles.
Tsoro ya sauko bisa kowane rai, kuma aka yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa ta wurin manzannin.
44 And all who believed were together, and had all things common.
Duka wadanda suka ba da gaskiya suna tare kuma komai nasu na kowanensu ne,
45 And they sold properties and possessions, and divided them to all, according as any man had need.
kuma suka saida kadarorinsu da mallakarsu kuma suka rarrabawa kowa, bisa ga irin bukatar da kowannensu yake da ita.
46 And continuing steadfastly, daily with one accord in the temple, and breaking bread from house to house, they partook of nourishment in gladness and evenness of heart,
A kowace rana suka cigaba tare da nufi daya a cikin haikali, suna kakkarya gurasa a gidaje, kuma suna raba abinci tsakaninsu cikin farin ciki da tawali'u a zuciya;
47 praising God, and having favor with the whole populace. And the Lord was adding to the church daily those being saved.
Suna yabon Allah kuma suna da tagomashi a gaban dukan mutane. Ubangiji kuma kullum yana kara masu wadanda suke samun ceto.

< Acts 2 >