< Acts 2 >
1 And while fulfilling the day of Pentecost, they were all together at the same place.
Da ranar Fentekos ta yi, dukansu suna tare wuri ɗaya.
2 And suddenly there developed a sound from the sky as of a forceful wind moving, and it filled the entire house where they were sitting.
Ba zato ba tsammani sai aka ji motsi kamar ta babbar iska tana hurowa daga sama ta kuma cika dukan gidan da suke zaune.
3 And there appeared to them dividing tongues, as of fire, and they settled upon each one of them.
Suka ga wani abin da ya yi kama da harsunan wuta, suka rarrabu suna kuma sassauka a kan kowannensu.
4 And they were all filled of the Holy Spirit, and began to speak with other tongues, as the Spirit gave them to declare.
Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka kuma fara magana da waɗansu harsuna yadda Ruhu ya sa suka iya.
5 Now there were dwelling at Jerusalem, Jews, devout men from every nation under heaven.
To, a Urushalima akwai Yahudawa masu tsoron Allah, daga kowace ƙasa a duniya.
6 And the sound of this that happened brought the multitude together. And it was bewildered because each one heard them speaking in his own language.
Da suka ji wannan motsi, taro ya haɗu wuri ɗaya a ruɗe, domin kowannensu ya ji suna magana da yarensa.
7 And they were amazed and marveled, saying to each other, Behold, are not all these men who speak Galileans?
Cike da mamaki, suka yi tambaya suna cewa, “Ashe, duk waɗannan mutane masu magana ba Galiliyawa ba ne?
8 And how do we each hear our own language in which we were born?
To, yaya kowannenmu yana ji suna yarensa?
9 Parthians and Medes and Elamites, and those dwelling in Mesopotamia, and Judea and Cappadocia, Pontus and Asia,
Fartiyawa, Medes da Elamawa; mazaunan Mesofotamiya, Yahudiya da Kaffadokiya, Fontus da Asiya,
10 and Phrygia and Pamphylia, Egypt and the parts of Libya along Cyrene, and those Roman aliens, including Jews and proselytes,
Firjiya da Famfiliya, Masar da sassa Libiya kusa da Sairin; baƙi daga Roma
11 Cretes and Arabians. We hear them speaking in our tongues the great things of God.
(Yahudawa da kuma waɗanda suka tuba suka shiga Yahudanci); Kiretawa da Larabawa, mun ji su suna shelar abubuwan banmamaki na Allah da yarenmu!”
12 And they were all amazed, and were perplexed, others saying to others, Whatever does this intend to be?
A ruɗe kuma cike da mamaki, suka tambayi junansu cewa, “Mene ne wannan yake nufi?”
13 But others, mocking said, They are filled of wine.
Duk da haka waɗansu suka yi musu ba’a suka ce, “Sun yi tatil da ruwan inabi ne.”
14 But Peter having stood up with the eleven, raised his voice and spoke out to them, saying, Jewish men, and all who dwell at Jerusalem, be this known to you, and listen to my sayings.
Sai Bitrus ya miƙe tsaye tare da Sha Ɗayan nan, ya ɗaga muryarsa ya yi wa taron jawabi ya ce, “’Yan’uwana Yahudawa da dukanku da kuke zama cikin Urushalima, bari in bayyana muku wannan, ku saurara da kyau ga abin da zan faɗa.
15 For these men are not drunken, as ye suppose, for it is the third hour of the day.
Waɗannan mutane ba su bugu ba, kamar yadda kuka ɗauka. Yanzu ƙarfe tara na safe ne kawai!
16 But this is that which was spoken through the prophet Joel:
A’a, ai, abin da aka yi magana ta bakin annabi Yowel ke nan cewa,
17 And it will be in the last days, says God, I will pour out from my Spirit upon all flesh. And your sons and your daughters will prophesy, and your young men will see visions, and your elders will dream dreams.
“Allah ya ce, ‘A kwanakin ƙarshe, zan zubo Ruhuna bisa dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, samarinku za su ga wahayoyi, dattawanku kuma za su yi mafarkai.
18 And also on my bondmen and on my bondmaids in those days I will pour out from my Spirit, and they will prophesy.
Kai, har ma a kan bayina, maza da mata, zan zubo Ruhuna a waɗancan kwanaki, za su kuwa yi annabci.
19 And I will give wonders in the heaven above, and signs on the earth beneath, blood, and fire, and vapor of smoke.
Zan nuna abubuwan banmamaki a sararin sama da alamu a nan ƙasa, jini da wuta da kuma hauhawan hayaƙi.
20 The sun will be changed into darkness, and the moon into blood, before that great and wonderful day of the Lord comes.
Za a mai da rana duhu, wata kuma ya zama jini, kafin zuwa rana mai girma da kuma ta ɗaukaka ta Ubangiji.
21 And it will be, that every man, whoever may call on the name of the Lord will be saved.
Kuma duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.’
22 Men, Israelites, hear ye these words. Jesus the Nazarene, a man shown by God among you by miracles and wonders and signs, which God did by him in the midst of you, as ye yourselves also know,
“Mutanen Isra’ila, ku saurari wannan. Yesu Banazare shi ne mutumin da Allah ya tabbatar muku ta wurin mu’ujizai, ayyukan banmamaki, da kuma alamu, waɗanda Allah ya yi a cikinku ta wurinsa, kamar yadda ku kanku kuka sani.
23 this man, having been designated (by the purpose and foreknowledge of God) a man delivered up, ye, having taken by lawless hands, killed, having crucified,
An ba da wannan mutum gare ku bisa ga nufin Allah da kuma rigyasaninsa, ku kuma tare da taimakon mugayen mutane, kuka kashe shi ta wurin kafa shi a kan gicciye.
24 whom God raised up, having loosed the pangs of death, because it was not possible for him to be held by it.
Amma Allah ya tashe shi daga matattu, ya’yantar da shi daga azabar mutuwa, don ba ya yiwuwa mutuwa ta riƙe shi.
25 For David speaks for him: I beheld the Lord always before me, because he is at my right hand, so that I may not be moved.
Dawuda ya yi faɗi game da shi cewa, “‘Kullum ina ganin Ubangiji a gabana. Gama yana a hannuna na dama, ba zan jijjigu ba.
26 Because of this my heart rejoiced, and my tongue was glad. And moreover my flesh will also rest in hope.
Saboda haka, zuciyata na farin ciki, harshena kuma na murna, jikina kuma zai kasance da bege,
27 Because thou will not leave my soul in Hades, nor will thou give thy Holy man to see decay. (Hadēs )
gama ba za ka bar ni cikin kabari ba, ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Hadēs )
28 Thou made known to me the paths of life. Thou will fill me of joy with thy countenance.
Ka sanar da ni hanyoyin rai, za ka cika ni da farin ciki a gabanka.’
29 Men, brothers, being permitted to speak to you with openness about the patriarch David, that he both perished and was buried, and his sepulcher is with us to this day.
“’Yan’uwa, zan iya tabbatar muku gabagadi cewa kakanmu Dawuda ya mutu aka kuma binne shi, kabarinsa kuwa yana a nan har yă zuwa yau.
30 Being therefore a prophet, and knowing that God had sworn with an oath to him, to raise the Christ from the fruit of his loins according to flesh to sit upon his throne.
Amma shi annabi ne ya kuma san abin da Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa zai ɗora ɗaya daga cikin zuriyarsa a kan gadon sarautarsa.
31 Having foreseen this, he spoke about the resurrection of the Christ, that his soul was not left behind in Hades, nor did his flesh see decay. (Hadēs )
Ganin abin da yake gaba, ya yi magana a kan tashin Kiristi daga matattu cewa, ba a bar shi a kabari ba, jikinsa kuma bai ruɓa ba. (Hadēs )
32 This Jesus, God raised up, of which we are all witnesses.
Allah ya tashe wannan Yesu zuwa rai, mu kuwa duk shaidu ne ga wannan.
33 Therefore, exalted by the right hand of God, and having received the promise of the Holy Spirit from the Father, he poured out this that ye now see and hear.
An ɗaukaka shi zuwa ga hannun dama na Allah, ya karɓi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga Uba, ya kuma zubo abin da yanzu kuke gani kuke kuma ji.
34 For David did not ascend into the heavens, but he himself says, The Lord said to my Lord, Sit thou at my right hand
Gama Dawuda bai hau zuwa sama ba, duk da haka ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
35 until I place thine enemies a footstool of thy feet.
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
36 Therefore let all the house of Israel know assuredly, that God has made him, this Jesus whom ye crucified, both Lord and Christ.
“Saboda haka bari dukan Isra’ila su tabbatar da wannan. Allah ya mai da wannan Yesu, da kuka gicciye, Ubangiji da kuma Kiristi.”
37 Now having heard this, they were pierced in the heart, and said to Peter and the other apostles, Men, brothers, what will we do?
Sa’ad da mutane suka ji wannan, sai suka soku a zuci sai suka ce wa Bitrus da sauran manzanni, “’Yan’uwa, me za mu yi?”
38 And Peter said to them, Repent ye, and be immersed each of you in the name of Jesus Christ for the remission of sins, and ye will receive the gift of the Holy Spirit.
Bitrus ya amsa, “Ku tuba a kuma yi muku baftisma, kowannenku a cikin sunan Yesu Kiristi domin gafarar zunubanku. Za ku kuwa karɓi kyautar Ruhu Mai Tsarki.
39 For the promise is to you, and to your children, and to all those in afar, as many as the Lord our God may call.
Alkawarin dominku ne da’ya’yanku da kuma dukan waɗanda suke da nesa, domin dukan waɗanda Ubangiji Allahnmu zai kira.”
40 And with many more other words he testified and exhorted them, saying, Be saved from this crooked generation.
Da waɗansu kalmomi masu yawa ya gargaɗe su; ya kuma roƙe su cewa, “Ku ceci kanku daga wannan lalataccen zamani.”
41 Indeed therefore those who received his word gladly, were immersed. And there were added in that day about three thousand souls.
Waɗanda suka yarda da saƙonsa kuwa aka yi musu baftisma, a ranar kuwa yawansu ya ƙaru da mutum kusan dubu uku.
42 And they were continuing steadfastly in the apostles doctrine, and in fellowship, and in the breaking of bread, and the prayers.
Suka ba da kansu ga koyarwar manzanni da kuma ga zumunci, ga gutsuttsura burodin da kuma ga addu’a.
43 And fear developed in every soul. And many wonders and signs occurred through the apostles.
Kowa ya cika da tsoro, manzannin kuwa suka aikata abubuwan banmamaki da alamu masu yawa.
44 And all who believed were together, and had all things common.
Dukan masu bi suna tare, suna kuma mallakar kome tare.
45 And they sold properties and possessions, and divided them to all, according as any man had need.
Suka dinga sayar da ƙaddarorinsu da kayayyakinsu, suka ba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
46 And continuing steadfastly, daily with one accord in the temple, and breaking bread from house to house, they partook of nourishment in gladness and evenness of heart,
Kowace rana suka ci gaba da taruwa a filin haikali. Suka gutsuttsura burodi a gidajensu suna cin abinci tare da farin ciki da zuciya ɗaya,
47 praising God, and having favor with the whole populace. And the Lord was adding to the church daily those being saved.
suna yabon Allah suna kuma samun tagomashin dukan mutane. Ubangiji kuwa ya ƙara yawansu kowace rana na waɗanda suke samun ceto.