< Acts 18 >

1 And after these things Paul having separated from Athens, he came to Corinth.
Bayan haka sai Bulus ya tafi Antakiya daga nan, ya wuce Korinti.
2 And having found a certain Jew named Aquila, a man of Pontus by origin, who recently came from Italy, and his wife Priscilla, because Claudius arranged for all the Jews to separate from Rome, he came to them.
A can ya sadu da wani Bayahude mai sunan Akila, dan kasar Buntus ne; bai dade da zuwa garin ba, daga Italiya ya zo da matarsa mai suna Balkisu, saboda Kalaudiyas ya ba da umarni dukan Yahudawa su bar Roma; sai Bulus ya je wurinsu.
3 And because he was of the same craft, he abode with them, and was working, for they were of the tentmakers craft.
Bulus ya zauna a gidansu don sana'arsu daya ce, wato, masu aikin Tanti ne.
4 And he was discoursing in the synagogue every sabbath, and was persuading Jews and Greeks.
Saboda haka Bulus na zuwa majami'a, yana yin nazari tare da su a kowace Asabaci. Yana kokari ya rinjayi Yahudawa da Helinawa.
5 And when both Silas and Timothy came down from Macedonia, Paul was being held by the Spirit, fully testifying to the Jews, Jesus the Christ.
Amma a lokacin da Sila da Timoti suka iso Makidoniya, Ruhu ya matsa Bulus ya shaida wa Yahudawa cewa Yesu Almasihu ne.
6 But when they opposed and slandered him, having shaken out his clothes, he said to them, Your blood is upon your heads. I am clean. From henceforth I will go to the Gentiles.
Lokacin da Yahudawa suka tayar masa suna zarginsa. Bulus ya kakkabe rigansa a gabansu yana cewa, “Alhakin jininku yana kanku; daga yanzu zan koma wurin al'ummai.”
7 And having departed from there, he went into the house of a certain man named Justus, who worships God, whose house was adjoining the synagogue.
Da ya bar wurinsu, ya tafi gidan Taitus Yustus mai wa Allah sujada. Gidansa na kusa da majami'a.
8 And Crispus, the synagogue ruler, believed in the Lord with his whole household, and many of the Corinthians who heard believed, and were immersed.
Kiristus shine shugaban majami'a, sai shi da dukan iyalin gidansa sun ba da gaskiya ga Ubangiji. Korantiyawa da yawa suka ji jawabin Bulus suka ba da gaskiya, aka yi masu Baftisma.
9 And the Lord spoke to Paul by a vision at night, Fear not, but speak, and be not silent,
Da dare Ubangiji ya ce wa Bulus a cikin wahayi, “Kada ka ji tsoro, amma ka yi magana kada kuma ka yi shuru.
10 because I am with thee, and no man will lay upon thee to harm thee, because many people are for me in this city.
Gama ina tare da kai, ba wanda zai cutar da kai, gama ina da mutane anan garin.”
11 And he remained a year and six months, teaching the word of God among them.
Bulus ya zauna a nan tsawon shekara daya da wata shida, yana koyar masu da maganar Allah.
12 But Gallio being proconsul of Achaia, the Jews with one accord attacked Paul and brought him to the judgment seat,
Amma da Galiyo ya samu zaman gwamnan Akaya, sai Yahudawa suka tayar wa Bulus har suka kai shi gaban dakalin shari'a.
13 saying, This man is persuading men to worship God against the law.
Suna cewa, “Wannan mutumin yana kokarin rinjayar mutane su yi sujadar da ta saba wa dokarmu.”
14 But when Paul was going to open his mouth, Gallio said to the Jews, If therefore indeed it were some crime or evil reckless deed, O ye Jews, I would have tolerated you according to the matter.
Duk da haka kafin Bulus ya yi magana, Galiyo ya ce wa Yahudawa, “Ku Yahudawa in da karar ku ta wani babban laifi ce wanda ya aikata, da sai in hukunta.
15 But if it is an issue about a word and names and the law from you, look ye yourselves, for I do not intend to be a judge of these things.
Amma tun da ya ke akan al'amurar, kalmomi ne, da ta sunaye da dokokin ku, ku je ku sasanta al'amuran ku.”
16 And he drove them from the judgment seat.
Galiyo ya kore su daga dakalin shari'a.
17 But all the Greeks, having taken Sosthenes the synagogue ruler, were beating him in front of the judgment seat. And Gallio was not going to judge, even of these things.
Saboda haka sai suka kama Sastanisu, suka yi masa duka sosai a gaban dakalin shari'a. Amma Galiyo bai damu da yadda suka karasa ba.
18 But Paul, who still remained considerable days with the brothers, having separated, sailed away to Syria (and with him Priscilla and Aquila), having shaved his head in Cenchrea, for he had a vow.
Bulus kuwa, bayan ya zauna tare da su na wasu kwanaki masu yawa, ya bar 'yan'uwan zuwa Suriya ta jirgin ruwa, tare da Balkisu da Akila. Kafin ya bar tashar jiragen ruwa da ke a Sankuriya, ya tafi saboda ya aske kansa, domin ya dauki alkawarin Banazare.
19 And he came to Ephesus and left behind those there, but having entered into the synagogue himself, he discoursed with the Jews.
Da suka iso Afisa, Bulus ya bar Balkisu da Akila anan. Shi kuwa ya shiga majami'ar Yahudawa yana nazari tare da su.
20 And when they asked him to remain on more time with them, he did not consent,
Da suka roki Bulus ya zauna da su na tsawon lokaci, bai yarda ba.
21 but separated from them, having said, I must definitely keep the coming feast at Jerusalem, but I will return again to you, God willing. And he launched from Ephesus.
Ya kama hanyarsa ya bar su ya ce, “In Allah ya yardar mani zan dawo wurinku wata rana.” Sai ya shiga jirgin ruwa daga Afisa.
22 And after coming down to Caesarea, having gone up and greeted the church, he went down to Antioch.
Daga saukar su a Kaisariya, sai ya haura zuwa Urushalima ya gai da iklisiya daga nan ya tafi Antakiya.
23 And after spending some time, he departed, passing through the region of Galatia and Phrygia, successively, strengthening all the disciples.
Bayan ya zauna na dan lokaci a wurin, Bulus ya kama hanyarsa zuwa yakin Galatiya da Firjiya anan ya karfafa almajirai.
24 Now a certain Jew named Apollos, an Alexandrian by origin, an eloquent man, came to Ephesus, being mighty in the scriptures.
A nan dai akwai wani Bayahude mai suna Afolos, dan asalin Iskandariya ne da haihuwa, ya zo Afisa. Shi masani ne a maganar Allah.
25 This was a man who was instructed in the way of the Lord. And being fervent in the Spirit, he was speaking and teaching accurately the things about the Lord, knowing only the immersion of John.
Afolos dai ya sami horo daga maganar Ubangiji. Shi mai kokari ne a ruhu, yana wa'azi da koyarwa daidai game da Yesu. Amma ya san da Baftismar Yahaya ne kadai.
26 And this man began to speak boldly in the synagogue, but when Aquila and Priscilla heard him, they took him aside, and expounded to him the way of God more accurately.
Afolos ya fara wa'azinsa da gabagadi a cikin majami'a. Da Balkisu da Akila suka ji shi sai suka yi abokantaka da shi, suka kara bayyana masa game da labarin hanyar Allah mafi daidai.
27 And when he intended to pass through into Achaia, the brothers wrote, having encouraged the disciples to receive him, who, when he arrived, assisted much those who believed through the grace.
Da ya so ya wuce zuwa cikin Akaya 'yan'uwa suka karfafa shi, sun rubuta wa almajiran da ke a Akaya, don su karbe shi da hannu biyu. Da ya iso wurinsu, ya kuwa karfafa 'yan'uwa da sun ba da gaskiya ta wurin alheri.
28 For he forcibly refuted the Jews in public, demonstrating by the scriptures Jesus to be the Christ.
Afolos ya ba Yahudawa mamaki da irin ikon da yake da shi da gwanintarsa, yadda yake nunawa daga nassoshi cewa Yesu shine Almasihu.

< Acts 18 >