< 2 John 1 >

1 The elder to the chosen lady and her children, whom I love in truth, and not only I, but also all those who know the truth,
Dattijon nan, Zuwa ga uwargida zaɓaɓɓiya da kuma’ya’yanta, waɗanda nake ƙauna ƙwarai da gaske kuma ba ni kaɗai ba, amma har da dukan waɗanda suka san gaskiya.
2 because of the truth that abides in us, and will be with us into the age. (aiōn g165)
Muna ƙaunarku saboda gaskiyan nan, wadda take cikinmu za tă kuma kasance tare da mu har abada. (aiōn g165)
3 Grace, mercy, peace will be with us from God the Father, and from the Lord Jesus Christ, the Son of the Father, in truth and love.
Alheri, jinƙai da kuma salama daga Allah Uba da kuma Yesu Kiristi, Ɗan Uba, su kasance tare da mu cikin gaskiya da ƙauna.
4 I rejoice exceedingly that I have found of thy children walking in truth, just as we received commandment from the Father.
Na yi farin ciki ƙwarai, da na sami waɗansu’ya’yanki suna tafiya cikin gaskiya, kamar yadda Uba ya umarce mu.
5 And now I beseech thee, lady, not as writing a new commandment to thee, but what we had from the beginning, that we would love each other.
Yanzu kuma, uwargida ƙaunatacciya, ba sabon umarni nake rubuta miki ba sai dai wanda muke da shi tun farko. Ina roƙo cewa mu ƙaunaci juna.
6 And this is love, that we should walk according to his commandments. This is the commandment, just as ye heard from the beginning, that ye should walk in it.
Ƙauna, ita ce mu yi biyayya ga umarnansa. Kamar yadda kuka ji tun da fari, umarninsa shi ne ku yi zaman ƙauna.
7 Because many deceivers have gone forth into the world, those not acknowledging Jesus Christ coming in flesh. This is the deceiver and the antichrist.
Masu ruɗi da yawa, waɗanda ba su yarda da zuwan Yesu Kiristi cikin jiki ba, sun riga sun fito a duniya. Duk irin mutumin nan mai ruɗi ne kuma magabcin Kiristi.
8 Watch yourselves, so that we may not lose what we have wrought, but may receive a full reward.
Ku lura don kada ku yi hasarar aikin da kuka yi, sai dai ku sami cikakken lada.
9 Every man transgressing, and not abiding in the doctrine of the Christ, does not have God. The man abiding in the doctrine of the Christ, this man has both the Father and the Son.
Duk mutumin da bai tsaya a kan koyarwar Kiristi ba, amma ya yi ƙari a kanta, mutumin nan ba shi da Allah. Amma wanda ya tsaya a kan koyarwar Kiristi, yana da Uban da kuma Ɗan.
10 If any man comes to you, and does not bring this doctrine, do not receive him into a house, and do not speak to him to rejoice.
Duk wanda ya zo wurinku bai kuma kawo koyarwan nan ba, kada ku karɓe shi a gidanku ko ku marabce shi.
11 For he who speaks to him to rejoice, partakes of his evil works.
Duk wanda ya karɓe shi yana tarayya da mugun aikinsa ke nan.
12 Having many things, I did not want to write to you by paper and ink, but I hope to come to you, and to speak mouth to mouth, so that our joy may be filled.
Ina da abubuwa da dama da zan rubuta muku, sai dai ba na so in yi amfani da takarda da inki in rubuta. A maimako, ina fata in ziyarce ku in kuma yi magana da ku fuska da fuska, domin farin cikinmu yă zama cikakke.
13 The children of thy chosen sister salute thee. Truly.
’Ya’yan’yar’uwarki wadda Allah ya keɓe, suna gaishe ku.

< 2 John 1 >