< 2 Corinthians 6 >

1 And working jointly, we urge you also not to receive the grace of God in vain
haka, tundashike muna aiki tare, na roke ku kar ku yi watsi da alherin Allah.
2 (for he says, At an acceptable time I heard thee, and in a day of salvation I helped thee. Behold, now is an acceptable time. Behold, now is a day of salvation),
Domin ya ce, “A lokacin alheri na saurare ku, kuma a ranar ceto na agaje ku.” Yanzu ne fa, lokacin alheri. Duba, yanzu ne ranar ceto.
3 giving not one cause of stumbling in anything, so that the ministry may not be criticized,
Ba mu sa sanadin faduwa a gaban kowannen ku, domin ba mu so hidimarmu ta zama marar amfani.
4 but in everything commending ourselves as helpers of God, in much perseverance, in afflictions, in necessities, in restrictions,
Maimakon haka, mun tabbatar da kan mu ta wurin dukan ayyukanmu, cewa mu bayin Allah ne. Mu bayinsa ne ta wurin yawan jimiri, azaba, kunci, wahala,
5 in stripes, in imprisonments, in tumults, in labors, in sleeplessness, in hungerings,
duka, kurkuku, tarzoma, cikin aiki tukuru, cikin rashin barci yawancin dare, cikin yunwa,
6 in purity, in knowledge, in longsuffering, in kindness, in the Holy Spirit, in non-hypocritical love,
cikin tsarki, ilimi, hakuri, kirki, cikin Ruhu Mai tsarki, da sahihiyar kauna.
7 in word of truth, in power of God, through the weapons of righteousness of the right hand and of the left,
Mu bayinsa ne cikin kalmar gaskiya, cikin ikon Allah. Muna kuma da makamai na adalci, a hanun dama da hagu.
8 through glory and disrepute, through slander and commendation; as deceitful, and yet true;
Muna aiki cikin daraja da rashin daraja, kushe da yabo. Ana zargin mu a kan mu mayaudara ne, duk da haka mu masu gaskiya ne.
9 as unknown, and well known; as dying, and behold, we live; as punished, and not put to death;
Muna aiki kamar ba a san mu ba, gashi kuwa mu sanannu ne. Muna aiki kamar masu mutuwa-duba! -har yanzu muna raye. Muna aiki kamar wadanda aka hukunta, amma ba hukuncin kisa ba.
10 as grieving, but always rejoicing; as poor, but making many rich; as having nothing, and yet possessing all things.
Muna aiki kamar muna bakinciki, amma a koyaushe muna farinciki. Muna aiki kamar matalauta, amma muna azurta mutane dayawa. Muna aiki kamar ba mu da komai, amma mun mallaki komai.
11 O Corinthians, our mouth has been opened to you, our heart has been enlarged.
Mun fada maku dukan gaskiyar, Korantiyawa, kuma zuciyar mu a bude ta ke.
12 Ye are not limited in us, but ye are limited in your bowels.
Ba mu kange zukatan ku ba, ku ne kuka kange zukatanku a gare mu.
13 But I speak the same recompense as to children, be ye also enlarged.
Yanzu a sabanin haka-Ina magana da ku kamar yara-ku bude mana zukatanku.
14 Do not become unequally yoked with unbelievers, for what partnership has righteousness and lawlessness? And what fellowship has light with darkness?
Kada ku yi cudanya da marasa bangaskiya. Wace tarayya ke tsakanin adalci da take shari'a? Ko kuma wace zumunta ce ke tsakanin haske da duhu?
15 And what agreement has Christ with Belial? Or what share have believers with non-believers?
Wace yarjejeniya ke tsakanin Almasihu da Ibilis? ko kuma me ya hada masu bangaskiya da marasa bangaskiya?
16 And what mutual agreement has a temple of God with idols? For ye are a temple of the living God, just as God said, I will dwell in them, and will walk among them. And I will be their God, and they will be a people to me.
ko wace yarjejeniya ce a tsakanin haikalin Allah da gumaka? Domin kuwa mu haikali ne na Allah mai rai, kamar yadda Allah ya ce: ''Zan zauna a cikin su, in kuma yi tafiya a tsakanin su. Zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.”
17 Therefore, Come ye out from among them, and be ye separated, says the Lord, And touch no unclean thing, and I will receive you
Sabili da haka, ''Ku fito daga cikin su, kuma ku zama kebabbu,'' in ji Ubangiji. ''Kada ku taba kazamin abu, zan kuma karbe ku.
18 and will be for a Father to you, and ye will be for sons and daughters to me, says the Lord Almighty.
Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama 'ya'ya maza da mata a gare ni,'' in ji Ubangiji Mai iko duka.

< 2 Corinthians 6 >