< 1 Peter 4 >

1 Therefore of Christ having suffered in flesh for us, arm ye yourselves also with the same mentality, because he who has suffered in flesh has ceased from sin,
Saboda haka, tunda yake Almasihu ya sha wuya a jiki, muma mu sha damara da wannan ra'ayi. Duk wanda ya sha wuya a jiki ya daina aikata zunubi.
2 in order to live the remaining time in flesh, no longer by lusts of men, but by the will of God.
Wannan mutum kuma baya kara zaman biye wa muguwar sha'awar mutumtaka, amma sai dai nufin Allah dukkan sauran kwanakinsa a duniya.
3 For enough time of life has past for you to accomplish the will of the Gentiles, having gone in debaucheries, lusts, excesses of wine, revelings, drinking parties, and lawless idolatries.
Gama lokaci ya wuce da zamu yi abin da al'ummai suke son yi, wato fajirci, mugayen sha'awace-sha'awace, da buguwa da shashanci da shaye-shaye da bautar gumaku da abubuwan kyama.
4 During which they think it strange of you not running together into the same pouring out of debauchery, while they slander.
Suna tunanin bakon abu ku ke yi da ba kwa hada kai tare da su yanzu a yin wadannan abubuwa, sai suna zarginku.
5 Men who will give back an accounting to him who fares readily to judge the living and the dead.
Za su bada lissafi ga wanda yake a shirye ya shari'anta masu rai da matattu.
6 For good news was preached even to the dead for this, so that they might indeed be judged according to men in flesh, but live according to God in spirit.
Shi yasa aka yi wa matattu wa'azin bishara, cewa ko da shike anyi masu shari'a cikin jikunan mutane, su rayu bisa ga Allah a ruhu.
7 But the end of all things has approached. Therefore be serious, and be sober for the prayers.
Karshen dukkan abubuwa yana gabatowa. Saboda haka, ku zama natsatsu, ku natsu cikin tunaninku domin yin addu'oi.
8 And above all having fervent love for yourselves, because love will cover a multitude of sins,
Gaba da kome, ku himmatu wajen kaunar juna, domin kauna bata neman tona zunuban wadansu.
9 stranger-loving toward each other without complaints.
Ku yi wa juna bakunta da abubuwa nagari ba tare da gunaguni ba.
10 As each has received a gift, serving it for yourselves, as good stewards of the manifold grace of God.
Yadda kowanne dayanku ya sami baiwa, kuyi amfani da su domin ku kyautata wa juna, kamar masu rikon amanar bayebaye na Allah, wanda ya ba mu hannu sake.
11 If any man speaks, as oracles of God. If any man serves, as of ability as God supplies. So that God may be glorified in all things through Jesus Christ, to whom is the glory and the dominion into the ages of the ages. Truly. (aiōn g165)
Idan wani yana yin wa'azi, ya zamana fadar Allah ya ke fadi, idan wani yana hidima, ya yi da karfin da Allah ya ba shi, domin cikin dukkan abubuwa a daukaka Allah ta wurin Yesu Almasihu. Daukaka da iko nasa ne har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
12 Beloved, ye should not be surprised at the fieriness in you, which occurs for a trial to you, like a strange thing happening to you.
Ya kaunatattu, kada ku zaci cewa matsananciyar wahalar da ta zo ta gwada ku bakon abu ne, ko kuma wani bakon abu ne yake faruwa a gareku.
13 But rejoice in so far as ye are partakers in the sufferings of the Christ, so that also at the revealing of his glory ye may rejoice, having exceeding joy.
Amma muddin kuna tarayya da Almasihu cikin wahalarsa, ku yi murna, domin kuyi farin ciki da murna sa'adda za a bayyana daukakarsa.
14 Blessed are ye if ye are reviled for the name of Christ, because the Spirit of glory and of God rests upon you. From them he is indeed blasphemed, but from you he is glorified.
Idan ana zargin ku sabili da sunan Almasihu, ku masu albarka ne, domin Ruhun daukaka da Ruhun Allah ya tabbata a kanku.
15 For let not any man of you suffer as a murderer, or a thief, or an evildoer, or as a busybody.
Amma kada kowannen ku ya sha wahala sabo da horon shi mai kisan kai ne, ko barawo, ko mamugunci, ko mai shisshigi.
16 But if as a Christian, let him not be ashamed, but let him glorify God in this regard.
Amma in wani yana shan wahala sabili da shi na Almasihu ne, kada ya ji kunya, amma ya daukaka Allah a wannan sunan.
17 Because the time to begin judgment is from the house of God, and if first from us, what is the end of those who disobey the good news of God?
Domin lokaci ya yi da shari'a za ta fara daga gidan iyalin Allah. Idan kuwa za a fara da mu, menene karshen wadanda suka ki biyayya da bisharar Allah?
18 And if the righteous man is scarcely saved, where will the irreverent and sinful man appear?
Idan mutum, “mai adalci ya tsira da kyar, to, me zai faru da marar bin Allah da mai zunubi kuma?”
19 Therefore also let those who suffer according to the will of God entrust their souls as to a faithful Creator by well-doing.
Sabo da haka bari wadanda suke shan wuya bisa ga nufin Allah, su mika rayukansu ga amintaccen Mahalicci suna kuma yin ayyuka nagari.

< 1 Peter 4 >