< 1 John 1 >

1 What was from the beginning, what we have heard, what we have seen with our eyes, what we looked upon, and our hands touched, concerning the Word of life
Abin nan da yake tun daga farko, wanda muka ji, wanda muka gani da idanunmu, wanda muka gani hannuwanmu suka kama, a wajen maganar rai.
2 (and the life was made known, and we have seen, and testify, and declare to you the eternal life that was with the Father, and was made known to us), (aiōnios g166)
Ran kuwa aka baiyyana shi, muka gani, muka bada shaida, muka gaya maku labarin rai na har abada, wanda da yake a wurin Uba, aka kuma sanar da mu. (aiōnios g166)
3 what we have seen and heard we also declare to you, so that ye also may have fellowship with us. Even also our fellowship with the Father, and with his Son Jesus Christ.
Wannan da muka gani muka ji muka baku labari, domin kuyi zumunci da mu, zumuncinmu kuwa tare da Uba yake da Dansa Yesu Almasihu.
4 And we write these things to you, so that our joy may be made full.
Haka nan, muna rubuta maku wadannan abubuwa domin farin cikinmu ya cika.
5 And this is the message that we have heard from him and declare to you, that God is light, and in him is no darkness at all.
Wannan shi ne sakon da muka ji daga wurinsa mu kuwa muka sanar da ku: Allah haske ne a wurinsa kuwa babu duhu ko kadan.
6 If we say that we have fellowship with him and walk in the darkness, we lie, and do not the truth.
Idan mun ce muna zumunci da shi kuma muna tafiya cikin duhu, muna yin karya kuma bama aikata gaskiya.
7 But if we walk in the light, as he is in the light, we have fellowship with each other, and the blood of Jesus Christ his Son cleanses us from every sin.
Amma idan muna tafiya cikin haske kamar yadda yake cikin haske, muna zumunci da juna, jinin Yesu Dansa ya wankemu daga dukka zunubi.
8 If we say that we have no sin, we lead ourselves astray, and the truth is not in us.
Idan mun ce bamu da zunubi, muna rudin kanmu kenan, ba kuma gaskiya a cikinmu.
9 If we confess our sins, he is faithful and righteous so that he will forgive us our sins, and cleanse us from every unrighteousness.
Amma idan mun fadi zunubanmu, shi mai aminci ne, mai adalci da zai gafarta mana zunubanmu, ya kuma wankemu daga dukkan rashin adalci.
10 If we say that we have not sinned, we make him a liar, and his word is not in us.
Idan mun ce bamu yi zunubi ba, mun mai da shi makaryaci kenan, maganarsa kuma bata cikinmu.

< 1 John 1 >