< 1 Corinthians 4 >
1 Thus let a man regard us as of helpers of Christ, and managers of mysteries of God.
Ga yadda za ku dauke mu, kamar bayin Almasihu da kuma masu rikon asiran Allah.
2 And beyond that, it is sought in managers that any man should be found faithful.
Hade da wannan, ana bukatar wakilai su zama amintattu.
3 But it is a very small thing to me that I might be appraised by you or by a day of mankind. Yet neither do I appraise myself,
Amma a gare ni, karamin abu ne ku yi mani shari'a, ko a wata kotu irin ta mutane. Gama bani yi wa kaina shari'a.
4 for I know nothing on myself. Yet I have not been made righteous in this, but he who appraises me is the Lord.
Ban sani ko akwai wani zargi a kaina ba, amma wannan bai nuna cewa bani da laifi ba. Ubangiji ne mai yi mani shari'a.
5 Therefore do not judge anything before the time, until the Lord comes who will both bring to light the hidden things of darkness, and make public the deliberations of the hearts. And then praise will come to each man from God.
Sabili da haka, kada ku yanke shari'a kafin lokaci, kafin Ubangiji ya dawo. Zai bayyana dukkan boyayyun ayyuka na duhu, ya kuma tona nufe-nufen zuciya. San nan kowa zai samu yabonsa daga wurin Allah.
6 Now these things, brothers, I applied to myself and Apollos for your sakes, so that in us ye might learn not to think above that which is written, so that ye may not be puffed up, one over the one against the other.
Yan'uwa, ina dora wadannan ka'idoji a kaina da Afollos domin ku, yadda ta wurin mu za ku koyi ma'anar maganar nan cewa, “kada ku zarce abin da aka rubuta.” Ya zama haka domin kada waninku ya kumbura yana nuna fifiko ga wani akan wani.
7 For who makes thee different? And what have thou that thou did not receive? And also if thou received it, why do thou boast as not having received it?
Gama wa yaga bambanci tsakanin ku da wasu? Me kuke da shi da ba kyauta kuka karba ba? Idan kyauta kuka karba, don me kuke fahariya kamar ba haka ba ne?
8 Already ye are filled. Already ye have become rich. Ye reigned without us, and O that ye did indeed reign, so that we also might reign with you.
Kun rigaya kun sami dukkan abubuwan da kuke bukata! Kun rigaya kun zama mawadata! Kun rigaya kun fara mulki- kuma ba tare da mu ba! Hakika, marmarina shine ku yi mulki, domin mu yi mulki tare da ku.
9 For I think God has exhibited us the apostles least, as men sentenced to die, because we became a spectacle to the world, both to agents and to men.
A tunanina, mu manzanni, Allah ya sa mu a jerin karshe kamar mutanen da aka zartar wa hukuncin mutuwa. Mun zama abin kallo ga duniya, ga mala'iku, ga mutane kuma.
10 We are foolish for the sake of Christ, but ye are wise in Christ. We are weak, but ye are strong. Ye are esteemed, but we are disreputable.
Mun zama marasa wayo sabili da Almasihu, amma ku masu hikima ne a cikin Almasihu. Mu raunana ne, amma ku masu karfi ne. Ana ganin mu marasa daraja, ku kuwa masu daraja.
11 As far as the present hour we both hunger, and thirst, and are ill clothed, and are treated roughly, and are homeless.
Har zuwa wannan sa'a, muna masu yunwa da kishi, marasa tufafi masu kyau, mun sha kazamin duka, kuma mun zama marasa gidaje.
12 And we toil, working with our own hands. Being reviled, we bless; being persecuted, we endure;
Mun yi fama sosai, muna aiki da hanuwanmu. Sa'adda an aibata mu, muna sa albarka. Sa'adda an tsananta mana, muna jurewa.
13 being slandered, we entreat. We became as trash of the world, an offscouring of all things, until now.
Sa'adda an zage mu, muna magana da nasiha. Mun zama, kuma har yanzu an dauke mu a matsayin kayan shara na duniya da abubuwa mafi kazamta duka.
14 I do not write these things shaming you, but I warn you as my beloved children.
Ban rubuta wadannan abubuwa domin in kunyata ku ba, amma domin in yi maku gyara kamar kaunatattun yayana.
15 For though ye have countless instructors in Christ, yet not many fathers. For in Christ Jesus I begot you through the good news.
Ko da kuna da masu riko dubu goma a cikin Almasihu, ba ku da ubanni da yawa. Gama ni na zama ubanku cikin Almasihu Yesu ta wurin bishara.
16 I beseech you therefore, become followers of me.
Don haka, ina kira gare ku da ku zama masu koyi da ni.
17 Because of this I sent Timothy to you, who is my beloved and faithful child in the Lord, who will remind you of my ways in Christ, just as I teach everywhere in every congregation.
Shiyasa na aiko Timoti wurin ku, kaunatacce da amintaccen dana cikin Ubangiji. Zai tunashe ku hanyoyina cikin Almasihu, kamar yadda nake koyar da su ko'ina da kowace Ikilisiya.
18 But as of me not coming to you, some men are puffed up.
Amma yanzu, wadansun ku sun zama masu fahariya, suna yin kamar ba zan zo wurinku ba.
19 But I will come to you shortly, if the Lord should will, and I will know, not the word of those who are puffed up, but the power.
Amma zan zo gare ku ba da dadewa ba, idan Ubangiji ya nufa. Sannan zan san fiye da maganar masu fahariya, amma kuma zan ga ikonsu.
20 For the kingdom of God is not in word, but in power.
Gama Mulkin Allah ba magana kadai ya kunsa ba, amma ya kunshi iko.
21 What do ye want? Should I come to you with a rod, or in love and a spirit of meekness?
Me kuke so? In zo wurin ku da sanda ne ko kuwa da kauna da ruhun nasiha?