< Psalmen 115 >
1 Niet ons, o HEERE! niet ons, maar Uw Naam geef eer, om Uwer goedertierenheid, om Uwer waarheid wil.
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 Waarom zouden de heidenen zeggen: Waar is nu hun God?
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 Onze God is toch in den hemel, Hij doet al wat Hem behaagt.
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 Hunlieder afgoden zijn zilver en goud, het werk van des mensen handen;
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 Zij hebben een mond, maar spreken niet; zij hebben ogen, maar zien niet;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 Oren hebben zij, maar horen niet; zij hebben een neus, maar zij rieken niet;
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 Hun handen hebben zij, maar tasten niet; hun voeten, maar gaan niet; zij geven geen geluid door hun keel.
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 Dat die hen maken hun gelijk worden, en al wie op hen vertrouwt.
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 Israel! vertrouw gij op den HEERE; Hij is hun Hulp en hun Schild.
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 Gij huis van Aaron! vertrouw op den HEERE; Hij is hun Hulp en hun Schild.
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 Gijlieden, die den HEERE vreest! vertrouwt op den HEERE; Hij is hun Hulp en hun Schild.
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 De HEERE is onzer gedachtig geweest, Hij zal zegenen; Hij zal het huis van Israel zegenen, Hij zal het huis van Aaron zegenen.
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 Hij zal zegenen, die den HEERE vrezen, de kleinen met de groten.
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 De HEERE zal den zegen over ulieden vermeerderen, over ulieden en over uw kinderen.
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 Gijlieden zijt den HEERE gezegend, Die den hemel en de aarde gemaakt heeft.
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 Aangaande den hemel, de hemel is des HEEREN; maar de aarde heeft Hij de mensenkinderen gegeven.
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 De doden zullen den HEERE niet prijzen, noch die in de stilte nedergedaald zijn.
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 Maar wij zullen den HEERE loven van nu aan tot in der eeuwigheid. Hallelujah!
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.