< Job 34 >
1 Verder antwoordde Elihu, en zeide:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Hoort, gij wijzen, mijn woorden, en gij verstandigen, neigt de oren naar mij.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Want het oor proeft de woorden, gelijk het gehemelte de spijze smaakt.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Laat ons kiezen voor ons, wat recht is; laat ons kennen onder ons wat goed is.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Want Job heeft gezegd: Ik ben rechtvaardig, en God heeft mijn recht weggenomen.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 Ik moet liegen in mijn recht; mijn pijl is smartelijk zonder overtreding.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Wat man is er, gelijk Job? Hij drinkt de bespotting in als water;
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 En gaat over weg in gezelschap met de werkers der ongerechtigheid, en wandelt met goddeloze lieden.
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Want hij heeft gezegd: Het baat een man niet, als hij welbehagen heeft aan God.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Daarom, gij, lieden van verstand, hoort naar mij: Verre zij God van goddeloosheid, en de Almachtige van onrecht!
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Want naar het werk des mensen vergeldt Hij hem, en naar eens ieders weg doet Hij het hem vinden.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Ook waarlijk, God handelt niet goddelooslijk, en de Almachtige verkeert het recht niet.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Wie heeft Hem gesteld over de aarde, en wie heeft de ganse wereld geschikt?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 Indien Hij Zijn hart tegen hem zette, zijn geest en zijn adem zou Hij tot Zich vergaderen;
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 Alle vlees zou tegelijk den geest geven, en de mens zou tot stof wederkeren.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Zo er dan verstand bij u is, hoor dit; neig de oren tot de stem mijner woorden.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Zou hij ook, die het recht haat, den gewonde verbinden, en zoudt gij den zeer Rechtvaardige verdoemen?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Zou men tot een koning zeggen: Gij Belial; tot de prinsen: Gij goddelozen!
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Hoe dan tot Dien, Die het aangezicht der vorsten niet aanneemt, en den rijke voor den arme niet kent? Want zij zijn allen Zijner handen werk.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 In een ogenblik sterven zij; zelfs ter middernacht wordt een volk geschud, dat het doorga; en de machtige wordt weggenomen zonder hand.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 Want Zijn ogen zijn op ieders wegen, en Hij ziet al zijn treden.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 Er is geen duisternis, en er is geen schaduw des doods, dat aldaar de werkers der ongerechtigheid zich verbergen mochten.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Gewisselijk, Hij legt den mens niet te veel op, dat hij tegen God in het gericht zou mogen treden.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Hij vermorzelt de geweldigen, dat men het niet doorzoeken kan, en stelt anderen in hun plaats.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Daarom dat Hij hun werken kent, zo keert Hij hen des nachts om, en zij worden verbrijzeld.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Hij klopt hen samen als goddelozen, in een plaats, waar aanschouwers zijn;
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 Daarom dat zij van achter Hem afgeweken zijn, en geen Zijner wegen verstaan hebben;
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 Opdat Hij op hem het geroep des armen brenge, en het geroep der ellendigen verhore.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Als Hij stilt, wie zal dan beroeren? Als Hij het aangezicht verbergt, wie zal Hem dan aanschouwen, zowel voor een volk, als voor een mens alleen?
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 Opdat de huichelachtige mens niet meer regere, en geen strikken des volks zijn.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Zekerlijk heeft hij tot God gezegd: Ik heb Uw straf verdragen, ik zal het niet verderven.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Behalve wat ik zie, leer Gij mij; heb ik onrecht gewrocht, ik zal het niet meer doen.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Zal het van u zijn, hoe Hij iets vergelden zal, dewijl gij Hem versmaadt? Zoudt gij dan verkiezen, en niet ik? Wat weet gij dan? Spreek.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 De lieden van verstand zullen met mij zeggen, en een wijs man zal naar mij horen;
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Dat Job niet met wetenschap gesproken heeft, en zijn woorden niet met kloek verstand geweest zijn.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 Mijn Vader, laat Job beproefd worden tot het einde toe, om zijner antwoorden wil onder de ongerechtige lieden.
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 Want tot zijn zonde zou hij nog overtreding bijvoegen; hij zou onder ons in de handen klappen, en hij zou zijn redenen vermenigvuldigen tegen God.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”