< Psalmen 105 >

1 Looft den HEERE, roept Zijn Naam aan, maakt Zijn daden bekend onder de volken.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Zingt Hem, psalmzingt Hem, spreekt aandachtelijk van al Zijn wonderen.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Roemt u in den Naam Zijner heiligheid; het hart dergenen, die den HEERE zoeken, verblijde zich.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Vraagt naar den HEERE en Zijn sterkte; zoekt Zijn aangezicht geduriglijk.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Gedenkt Zijner wonderen, die Hij gedaan heeft, Zijner wondertekenen, en der oordelen Zijns monds.
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 Gij zaad van Abraham, Zijn knecht, gij kinderen van Jakob, Zijn uitverkorene!
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Hij is de HEERE, onze God; Zijn oordelen zijn over de gehele aarde.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Hij gedenkt Zijns verbonds tot in der eeuwigheid, des woords, dat Hij ingesteld heeft, tot in duizend geslachten;
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 Des verbonds, dat Hij met Abraham heeft gemaakt, en Zijns eeds aan Izak;
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 Welken Hij ook gesteld heeft aan Jakob tot een inzetting, aan Israel tot een eeuwig verbond,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 Zeggende: Ik zal u geven het land Kanaan, het snoer van ulieder erfdeel.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Als zij weinig mensen in getal waren, ja, weinig en vreemdelingen daarin;
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 En wandelden van volk tot volk, van het ene koninkrijk tot het andere volk;
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 Hij liet geen mens toe hen te onderdrukken; ook bestrafte Hij koningen om hunnentwil, zeggende:
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 Tast Mijn gezalfden niet aan, en doet Mijn profeten geen kwaad.
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Hij riep ook een honger in het land; Hij brak allen staf des broods.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Hij zond een man voor hun aangezicht henen; Jozef werd verkocht tot een slaaf.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 Men drukte zijn voeten in den stok; zijn persoon kwam in de ijzers.
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 Tot den tijd toe, dat Zijn woord kwam, heeft hem de rede des HEEREN doorlouterd.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 De koning zond, en deed hem ontslaan; de heerser der volken liet hem los.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 Hij zette hem tot een heer over zijn huis, en tot een heerser over al zijn goed;
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 Om zijn vorsten te binden naar zijn lust, en zijn oudsten te onderwijzen.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Daarna kwam Israel in Egypte, en Jakob verkeerde als vreemdeling in het land van Cham.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 En Hij deed Zijn volk zeer wassen, en maakte het machtiger dan Zijn tegenpartijders.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 Hij keerde hun hart om, dat zij Zijn volk haatten, dat zij met Zijn knechten listiglijk handelden.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Hij zond Mozes, Zijn knecht, en Aaron, dien Hij verkoren had.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 Zij deden onder hen de bevelen Zijner tekenen, en de wonderwerken in het land van Cham.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Hij zond duisternis, en maakte het duister; en zij waren Zijn woord niet wederspannig.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 Hij keerde hun wateren in bloed, en Hij doodde hun vissen.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 Hun land bracht vorsen voort in overvloed, tot in de binnenste kameren hunner koningen.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 Hij sprak, en er kwam een vermenging van ongedierte, luizen, in hun ganse landpale.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 Hij maakte hun regen tot hagel, vlammig vuur in hun land.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 En Hij sloeg hun wijnstok en hun vijgeboom, en Hij brak het geboomte hunner landpalen.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 Hij sprak, en er kwamen sprinkhanen en kevers, en dat zonder getal;
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 Die al het kruid in hun land opaten, ja, aten de vrucht hunner landouwe op.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Hij versloeg ook alle eerstgeborenen in hun land, de eerstelingen al hunner krachten.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 En Hij voerde hen uit met zilver en goud; en onder hun stammen was niemand, die struikelde.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 Egypte was blijde, als zij uittrokken, want hun verschrikking was op hen gevallen.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Hij breidde een wolk uit tot een deksel, en vuur om den nacht te verlichten.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 Zij baden, en Hij deed kwakkelen komen, en Hij verzadigde hen met hemels brood.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 Hij opende een steenrots, en er vloeiden wateren uit, die gingen door de dorre plaatsen als een rivier.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 Want Hij dacht aan Zijn heilig woord, aan Abraham, Zijn knecht.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 Alzo voerde Hij Zijn volk uit met vrolijkheid, Zijn uitverkorenen met gejuich.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 En Hij gaf hun de landen der heidenen, zodat zij in erfenis bezaten den arbeid der volken;
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 Opdat zij Zijn inzettingen onderhielden, en Zijn wetten bewaarden. Hallelujah!
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Psalmen 105 >