< Spreuken 2 >

1 Mijn zoon! zo gij mijn redenen aanneemt, en mijn geboden bij u weglegt;
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 Om uw oren naar wijsheid te doen opmerken; zo gij uw hart tot verstandigheid neigt;
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 Ja, zo gij tot het verstand roept, uw stem verheft tot de verstandigheid;
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 Zo gij haar zoekt als zilver, en naspeurt als verborgen schatten;
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 Dan zult gij de vreze des HEEREN verstaan, en zult de kennis van God vinden.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Want de HEERE geeft wijsheid; uit Zijn mond komt kennis en verstand.
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 Hij legt weg voor de oprechten een bestendig wezen; Hij is een Schild dengenen, die oprechtelijk wandelen;
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 Opdat zij de paden des rechts houden; en Hij zal den weg Zijner gunstgenoten bewaren.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Dan zult gij verstaan gerechtigheid, en recht, en billijkheden, en alle goed pad.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 Als de wijsheid in uw hart zal gekomen zijn, en de wetenschap voor uw ziel zal liefelijk zijn;
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Zo zal de bedachtzaamheid over u de wacht houden, de verstandigheid zal u behoeden;
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 Om u te redden van den kwaden weg, van den man, die verkeerdheden spreekt;
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 Van degenen, die de paden der oprechtheid verlaten, om te gaan in de wegen der duisternis;
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 Die blijde zijn in het kwaad doen, zich verheugen in de verkeerdheden des kwaden;
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 Welker paden verkeerd zijn, en afwijkende in hun sporen;
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 Om u te redden van de vreemde vrouw, van de onbekende, die met haar redenen vleit;
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 Die den leidsman harer jonkheid verlaat, en het verbond haars Gods vergeet;
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 Want haar huis helt naar den dood, en haar paden naar de overledenen.
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 Allen die tot haar ingaan, zullen niet wederkomen, en zullen de paden des levens niet aantreffen;
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 Opdat gij wandelt op den weg der goeden, en houdt de paden der rechtvaardigen.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 Want de vromen zullen de aarde bewonen, en de oprechten zullen daarin overblijven;
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 Maar de goddelozen zullen van de aarde uitgeroeid worden, en de trouwelozen zullen er van uitgerukt worden.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.

< Spreuken 2 >