< Job 18 >

1 Toen antwoordde Bildad, de Suhiet, en zeide:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Hoe lang is het, dat gijlieden een einde van woorden zult maken? Merkt op, en daarna zullen wij spreken.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Waarom worden wij geacht als beesten, en zijn onrein in ulieder ogen?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 O gij, die zijn ziel verscheurt door zijn toorn! Zal om uwentwil de aarde verlaten worden, en zal een rots versteld worden uit haar plaats?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Ja, het licht der goddelozen zal uitgeblust worden, en de vonk zijns vuurs zal niet glinsteren.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 Het licht zal verduisteren in zijn tent, en zijn lamp zal over hem uitgeblust worden.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 De treden zijner macht zullen benauwd worden, en zijn raad zal hem nederwerpen.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Want met zijn voeten zal hij in het net geworpen worden, en zal in het wargaren wandelen.
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 De strik zal hem bij de verzenen vatten; de struikrover zal hem overweldigen.
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 Zijn touw is in de aarde verborgen, en zijn val op het pad.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 De beroeringen zullen hem rondom verschrikken, en hem verstrooien op zijn voeten.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 Zijn macht zal hongerig wezen, en het verderf is bereid aan zijn zijde.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 De eerstgeborene des doods zal de grendelen zijner huid verteren, zijn grendelen zal hij verteren.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Zijn vertrouwen zal uit zijn tent uitgerukt worden; zulks zal hem doen treden tot den koning der verschrikkingen.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 Zij zal wonen in zijn tent, waar zij de zijne niet is; zijn woning zal met zwavel overstrooid worden.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 Van onder zullen zijn wortelen verdorren, en van boven zal zijn tak afgesneden worden.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Zijn gedachtenis zal vergaan van de aarde, en hij zal geen naam hebben op de straten.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 Men zal hem stoten van het licht in de duisternis, en men zal hem van de wereld verjagen.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 Hij zal geen zoon, noch neef hebben onder zijn volk; en niemand zal in zijn woningen overig zijn.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Over zijn dag zullen de nakomelingen verbaasd zijn, en de ouden met schrik bevangen worden.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Gewisselijk, zodanige zijn de woningen des verkeerden, en dit is de plaats desgenen die God niet kent.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”

< Job 18 >