< Psalmen 48 >
1 Een lied; een psalm van de zonen van Kore. Groot is Jahweh, hoog geprezen In de stad van onzen God!
Waƙa ce. Zabura ta’ya’yan Kora maza. Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.
2 Lieflijk verheft zich zijn heilige berg, Voor heel de aarde een vreugde. De Sionsberg is de Spits van het Noorden, De stad van een machtigen Koning;
Kyakkyawa ce cikin tsayinta, abin farin cikin dukan duniya. Kamar ƙwanƙoli mafi tsayi na Zafon ne Dutsen Sihiyona, birnin Babban Sarki.
3 God woont in haar burchten, En toont zich een veilige schuts.
Allah yana cikin fadodinta; ya nuna kansa mafaka ce gare ta.
4 Want zie, de koningen hadden zich met elkander verbonden, En rukten gezamenlijk aan;
Sa’ad da sarakuna suka haɗa rundunoni, sa’ad da suka yi gaba tare,
5 Maar toen ze haar zagen, stonden ze stom van ontzetting, En stoven verschrokken uiteen.
sun gan ta suka kuwa yi mamaki; suka gudu don tsoro.
6 Vreselijke angst greep hen aan, En wee als een barende vrouw:
Rawar jiki ya kama su a can, zafi kamar na mace mai naƙuda.
7 Ineens als een storm uit het oosten, Die de Tarsjisj-schepen vernielt.
Ka hallaka su kamar jiragen ruwan Tarshish da iskar gabas ta wargaje.
8 Wat we vroeger hadden gehoord, Hebben we nu ook gezien: Jahweh der heirscharen woont in de stad, Onze God woont in de stad, en laat haar eeuwig bestaan!
Yadda muka ji, haka muka gani a cikin birnin Ubangiji Maɗaukaki, a cikin birnin Allahnmu. Allah ya sa ta zauna lafiya har abada. (Sela)
9 Wij gedenken uw goedheid, o God, Binnen uw tempel.
Cikin haikalinka, ya Allah, mun yi tunani a kan ƙaunarka marar ƙarewa.
10 Uw lof, o God, reikt als uw Naam Tot aan de grenzen der aarde. Vol gerechtigheid is uw rechterhand,
Kamar sunanka, ya Allah, yabonka ya kai iyakokin duniya; hannunka na dama ya cika da adalci.
11 Sions berg is er over verheugd; En Juda’s dochteren juichen van vreugde, O Jahweh, om uw gericht.
Dutsen Sihiyona ya yi farin ciki, ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukuntanka.
12 Trekt rond de Sion, loopt er omheen: Telt zijn torens,
Yi tafiya cikin Sihiyona, ku kewaye ta, ku ƙirga hasumiyoyinta,
13 Let op zijn wallen Ziet naar zijn burchten; Om aan een volgend geslacht te vertellen,
ku lura da katangarta da kyau, ku dubi fadodinta, don ku faɗe su ga tsara mai zuwa.
14 Dat God hier woont, Dat onze God ons leidt Voor eeuwig en immer!
Gama wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin; zai zama jagorarmu har zuwa ƙarshe.