< Psalmen 37 >

1 Van David. Wees niet afgunstig op zondaars, En benijd de boosdoeners niet;
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 Want snel versmachten zij als gras, Verkwijnen als het groen gewas.
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 Vertrouw op Jahweh, doe enkel wat goed is, Blijf in het land en wees trouw;
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 Dan zult gij uw vreugde in Jahweh vinden, En Hij schenkt u wat uw hart maar begeert.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 Laat Jahweh uw weg maar bestieren, Verlaat u op Hem: Hij zal hem banen;
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 Als de dageraad doet Hij uw gerechtigheid stralen, En als de middagzon uw recht.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 Berust in Jahweh, En blijf op Hem hopen. Benijd niet den man, wien het goed gaat, Ofschoon hij bedriegt.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 Word niet toornig en maak u niet boos, Wind u niet op: gij maakt het maar erger;
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 Want de zondaars worden vernietigd, Maar die op Jahweh vertrouwen, bezitten het Land!
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 Een ogenblik maar: en de zondaar is er niet meer; Gij zoekt naar zijn plaats: hij is weg.
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 Maar de rechtschapenen bezitten het Land, En genieten een heerlijke vrede.
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 De zondaar belaagt den rechtvaardige, En knarst tegen hem op zijn tanden;
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 Maar de Heer lacht hem uit, Want Hij ziet zijn Dag al nabij.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 De bozen trekken hun zwaard en spannen hun boog, Om ongelukkigen en armen te doden, en vromen te slachten;
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 Maar het zwaard dringt in hun eigen hart, En hun bogen worden gebroken.
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 Beter het weinige, dat de rechtvaardige heeft, Dan de geweldige rijkdom der bozen;
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 Want de arm der bozen wordt gebroken, Maar voor de rechtvaardigen is Jahweh een stut.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 Jahweh zorgt voor de dagen der vromen, En hun erfdeel blijft eeuwig bijeen;
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 Ze staan niet verlegen in tijden van rampspoed, Maar worden verzadigd bij hongersnood.
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 Maar de goddelozen gaan zeker te gronde, En hun kinderen bedelen om brood; Jahweh’s vijanden vergaan als de glorie der velden, En verdwijnen als rook.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 De boze moet lenen, en kan niet betalen, De gerechte kan mild zijn en geven;
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 Want wien Hij zegent, bezit het Land, Maar wien Hij vervloekt, wordt vernietigd.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 Jahweh leidt de schreden der mensen, Hij richt overeind, wiens gedrag Hem behaagt;
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 En mocht hij al wankelen, toch zal hij niet vallen, Want Jahweh houdt hem bij de hand.
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 Ik was jong, en nu ben ik oud: Maar nooit heb ik een vrome verlaten gezien;
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 Steeds kan hij nog mild zijn en aan anderen lenen, Zijn nageslacht tot zegen zijn.
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 Houd u ver van het kwaad, en doe enkel wat goed is, Dan woont gij veilig voor eeuwig;
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 Want Jahweh heeft de gerechtigheid lief, En nimmer verlaat Hij zijn vromen. De bozen worden voor eeuwig vernietigd, En het geslacht van de zondaars vergaat;
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 Maar de rechtvaardigen bezitten het Land, En blijven er altijd in wonen.
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 De mond van den rechtvaardige verkondigt de wijsheid, En zijn tong spreekt wat recht is.
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 Hij draagt de Wet van zijn God in zijn hart; Nooit wankelen zijn schreden.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 De boze loert op den vrome, En zoekt hem te doden;
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 Maar Jahweh laat hem niet in zijn macht, En duldt geen veroordeling, als men hem richt.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 Blijf op Jahweh vertrouwen, En bewandel zijn wegen; Dan stelt Hij u in het bezit van het Land, En zult gij de verdelging der zondaars aanschouwen.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 Ik heb een zondaar gezien in zijn vermetele trots, Hoog als een Libanon-ceder;
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 Ik ging voorbij: zie, hij was er niet meer; Ik zocht hem, hij was niet te vinden.
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 Geef acht op den vrome en let op den brave: Het kroost van dien man leeft in vrede;
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 Maar de zondaars gaan allen te gronde, De kinderen der bozen worden vernietigd.
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 Jahweh is het heil van de vromen, Hun toevlucht in tijden van nood;
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 Jahweh helpt en beschermt hen tegen de bozen, Hij redt hen, als ze vluchten tot Hem!
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.

< Psalmen 37 >