< Psalmen 2 >

1 Waarom razen de volken, Bluffen de naties,
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
2 Komen de koningen der aarde bijeen, Spannen de vorsten samen tegen Jahweh en zijn Gezalfde:
Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
3 "Laat ons hun ketens verbreken, Ons van hun boeien ontslaan!"
Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
4 Die in de hemelen woont, lacht hen uit, Jahweh bespot ze;
Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
5 Dan dreigt Hij ze toornig, Doet ze rillen voor zijn gramschap:
Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
6 "Ik zelf stel Mij een koning aan, Op Sion, mijn heilige berg!"
“Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
7 Nu wil Ik Jahweh’s beslissing verkonden; Hij heeft Mij gezegd: Gij zijt mijn Zoon; Ik heb U heden verwekt.
Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
8 Vraag Mij: dan geef Ik U de volkeren tot erfdeel, En de grenzen der aarde tot uw bezit;
Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
9 Gij moogt ze vermorzelen met ijzeren knots, En stuk slaan als een aarden pot.
Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
10 Koningen, bedenkt het dus wel; Weest gewaarschuwd, wereldregeerders!
Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
11 Dient Jahweh in vreze; Beeft, en kust Hem de voeten!
Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
12 Anders ontsteekt Hij in toorn, en loopt gij uw verderf tegemoet, Want licht kan zijn gramschap ontvlammen. Gelukkig, wie tot Hem zijn toevlucht neemt!
Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.

< Psalmen 2 >