< Psalmen 135 >

1 Halleluja! Looft Jahweh’s Naam, Looft Hem, dienaars van Jahweh:
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 Gij, die in het huis van Jahweh staat, In de voorhoven van het huis van onzen God!
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Looft Jahweh: want Jahweh is goed, Verheerlijkt zijn Naam: want die is zo lieflijk;
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 Want Jahweh heeft Zich Jakob verkoren, En Israël tot zijn bezit!
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 Ja, ik weet het: Jahweh is groot, Onze Heer boven alle goden verheven;
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Jahweh doet wat Hij wil In hemel en aarde, in zeeën en diepten.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 Hij laat de wolken verrijzen Aan de kimmen der aarde; Smeedt de bliksem tot regen, Haalt de wind uit zijn schuren.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 Hij was het, die Egypte’s eerstgeborenen sloeg, Van mensen en vee;
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 Die tekenen en wonderen deed in uw midden, Egypte, Tegen Farao en al die hem dienden;
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 Die talrijke volken versloeg, En machtige koningen doodde:
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Sichon, den vorst der Amorieten, En Og, den koning van Basjan. Hij was het, die alle vorsten vernielde En alle koninkrijken van Kanaän;
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 En die hun land ten erfdeel gaf, Tot bezit aan Israël, zijn volk.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Uw Naam duurt eeuwig, o Jahweh, Uw roem, o Jahweh, van geslacht tot geslacht;
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 Want Jahweh schaft recht aan zijn volk, En ontfermt Zich over zijn dienaars.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 Maar de goden der volken zijn zilver en goud, Door mensenhanden gemaakt:
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 Ze hebben een mond, maar kunnen niet spreken; Ogen, maar kunnen niet zien;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 Oren, maar kunnen niet horen; Ze hebben geen adem in hun mond.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 Aan hen worden gelijk, die ze maken, En allen, die er op hopen!
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 Huis van Israël, zegent dan Jahweh; Huis van Aäron, zegent dan Jahweh;
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 Huis van Levi, zegent dan Jahweh; Die Jahweh vrezen, zegent dan Jahweh;
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Gezegend zij Jahweh uit Sion, Hij, die in Jerusalem woont!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psalmen 135 >