< Psalmen 109 >
1 Voor muziekbegeleiding. Een psalm van David. Mijn God, tot wien mijn loflied klinkt, Zwijg toch niet stil!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 Want men zet een mond vol boosheid en bedrog tegen mij op, En belastert mij met leugentongen;
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 Men bestookt mij met woorden van haat, En bestrijdt mij zonder enige grond;
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 Men belaagt mij tot loon voor mijn liefde, En tot loon voor mijn bidden;
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 Men vergeldt mij kwaad voor goed, En haat voor mijn liefde.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Stel een gewetenloos rechter over hem aan, En aan zijn rechterhand trede een valse aanklager op;
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 Voor het gerecht worde hij schuldig bevonden, En smeke hij tevergeefs om genade.
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Mogen zijn dagen maar kort zijn, En zijn ambt aan een ander vervallen.
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Zijn kinderen mogen wezen, Zijn vrouw een weduwe worden;
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Mogen zijn zonen als bedelaars zwerven, Zelfs uit hun krotten worden verjaagd.
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 De woekeraar legge beslag op heel zijn bezit, En vreemden mogen met zijn verdiensten gaan strijken.
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 Laat niemand zich zijner ontfermen, Niemand zich over zijn wezen erbarmen;
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Laat zijn kroost ten ondergang worden gedoemd, Zijn naam al verdwijnen in het eerste geslacht.
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Moge Jahweh de misdaad zijner vaderen gedenken, En de schuld van zijn moeder nooit worden gedelgd;
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 Jahweh houde ze altijd voor ogen, Zodat zelfs hun aandenken van de aarde verdwijnt.
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 Want hij dacht er niet aan, barmhartig te zijn, Maar vervolgde den ellendige, arme en bedroefde ten dode.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 Hij hield van vervloeking: die treffe hem dan; Geen zegen wilde hij spreken: die blijve hem verre!
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 De vloek trok hij aan als een kleed: Die dringe hem als water in het lijf, als olie in zijn gebeente;
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 Die worde de mantel, waarin hij zich hult, De gordel, die hij altijd moet dragen.
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Zó moge Jahweh mijn haters vergelden, En die laag van mij lasteren!
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 Maar treed Gìj voor mij op, o Jahweh, mijn Heer, En red mij omwille van uw Naam naar de rijkdom uwer genade!
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Want ik ben arm en ellendig, En mijn hart krimpt ineen in mijn borst;
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 Ik zink weg als een verdwijnende schaduw, Word voortgejaagd als een sprinkhanenzwerm;
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 Van het vasten knikken mijn knieën, En mijn vermagerd lichaam schrompelt ineen.
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 Zó ben ik hun een bespotting geworden; Die mij zien, schudden meewarig het hoofd.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Help mij, Jahweh, mijn God, En red mij naar uw genade;
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 Opdat men erkenne, dat het uw hand is, Jahweh: dat Gij het volbracht!
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Laat hèn dan maar vloeken, als Gìj mij wilt zegenen; Mijn vijand zich schamen, maar uw knecht zich verheugen;
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Mogen mijn tegenstanders met smaad worden bekleed, En zich in hun schande hullen als in een mantel!
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 Dan zal ik Jahweh juichend danken, En voor een talloze schare Hem prijzen;
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 Omdat Hij aan de rechterhand van den ongelukkige staat, Om hem te redden, van die hem verdoemen!
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.