< Psalmen 106 >

1 Halleluja! Looft Jahweh, want Hij is goed En zijn genade duurt eeuwig!
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Wie kan Jahweh’s machtige daden vermelden, En heel zijn glorie verkonden?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Gelukkig hij, die de wet onderhoudt, En altijd het goede blijft doen!
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Wees ons indachtig, o Jahweh, Om uw liefde voor uw volk; Zoek ons op met uw heil,
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 Opdat wij het geluk uwer vrienden aanschouwen, Met uw blijde volk ons verblijden, Met uw erfdeel mogen roemen!
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Ach, wij hebben gezondigd met onze vaderen, Wij hebben misdreven en kwaad gedaan!
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Onze vaderen in Egypte Hebben al niet op uw wonderen gelet; En zonder aan uw talrijke gunsten te denken, Zich bij de Rode Zee tegen den Allerhoogste verzet!
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Toch redde Hij hen om wille van zijn Naam, En om zijn almacht te tonen:
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 Hij bedreigde de Rode Zee, ze liep droog, Hij leidde hen tussen de golven als door een uitgedroogd land.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 Hij redde hen uit de hand van hun haters, Verloste hen uit de macht van hun vijand;
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 De wateren spoelden over hun vijanden heen, En geen bleef er over!
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Toen sloegen ze geloof aan zijn woorden, En zongen zijn lof.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Maar spoedig waren ze weer zijn werken vergeten, En wachtten zijn raadsbesluiten niet af;
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 Ze gaven zich in de woestijn aan hun gulzigheid over, En stelden God op de proef in de steppe.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Hij schonk hun wat ze Hem vroegen, Maar Hij liet ze er spoedig van walgen.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 Daarna werden ze in hun kamp afgunstig op Moses, En op Aäron, aan Jahweh gewijd.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 Maar de aarde spleet open, zwolg Datan in, En bedolf de bent van Abiram;
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 Vuur verbrandde hun aanhang, Vlammen verteerden de bozen!
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Dan maakten ze een kalf bij de Horeb, En wierpen zich voor een afgietsel neer;
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 Ze verruilden hun Glorie Voor het beeld van een grasvretend rund.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 Ze vergaten God, hun Verlosser Die grote dingen in Egypte had gedaan,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 Wonderwerken in het land van Cham, Ontzaglijke daden bij de Rode Zee.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 En zeker had Hij hun verdelging beslist, Als Moses, zijn geliefde, er niet was geweest; Maar deze stelde zich tegen Hem in de bres, Om Hem te weerhouden, hen in zijn toorn te vernielen.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Later versmaadden ze het heerlijke land, En sloegen geen geloof aan zijn woord;
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 Ze begonnen in hun tenten te morren, En luisterden niet naar Jahweh’s stem.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Toen stak Hij zijn hand tegen hen op: Hij zou ze neerslaan in de woestijn,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 Hun zaad verstrooien onder de volken, Ze over vreemde landen verspreiden!
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 Dan weer koppelden ze zich aan Báal-Peor, En aten de offers van levenloze wezens;
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Ze tergden Hem door hun gedrag, Zodat er een slachting onder hen woedde.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Toen trad Pinechas op, om de misdaad te wreken, En de slachting hield op;
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 Het werd hem tot verdienste gerekend, Van geslacht tot geslacht voor altijd.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 Ook bij de wateren van Meriba hebben ze Hem getergd, En ging het Moses om hunnentwil slecht:
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 Want ze hadden zijn stemming verbitterd, Zodat hem onbezonnen woorden ontsnapten.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 Ook verdelgden ze de volkeren niet, Zoals Jahweh het hun had bevolen;
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 Maar ze vermengden zich met de heidenen, En leerden hun gewoonten aan:
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 Ze vereerden hun beelden, en die werden hun strik;
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Ze brachten hun zonen en dochters aan de goden ten offer;
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 Ze gingen onschuldig bloed vergieten, Het bloed van hun zonen en dochters; Ze offerden het aan de beelden van Kanaän, En het land werd door hun bloedschuld ontwijd.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Zo bezoedelden ze zich door eigen maaksels, En dreven overspel met het werk hunner handen!
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Toen werd Jahweh vergramd op zijn volk, En zijn erfdeel begon Hem te walgen:
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 Hij leverde ze aan de heidenen uit, En hun haters werden hun meesters;
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Ze werden verdrukt door hun vijand, Moesten bukken onder hun macht.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 En al bracht Hij hun telkens verlossing, Ze bleven in hun opstand volharden! Maar werden ze door hun misdaad vermorzeld,
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Dan zag Hij neer op hun nood, zodra Hij hun smeken vernam;
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 Dan was Hij voor hen zijn verbond weer indachtig, Had deernis met hen naar zijn grote ontferming;
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 Dan liet Hij hen genade vinden, Bij die hen hadden weggevoerd.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Ach, red ons Jahweh, onze God, En breng ons uit het land der heidenen samen: Opdat wij uw heilige Naam mogen danken, En uw heerlijkheid prijzen!
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Gezegend zij Jahweh, Israëls God, van eeuwigheid tot eeuwigheid! Laat heel het volk het herhalen: Amen! Halleluja!
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< Psalmen 106 >