< Spreuken 1 >
1 Spreuken van Salomon, den zoon van David, Den koning van Israël:
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 Ze leren u kennen wijsheid en tucht, Ze geven u begrip voor verstandige woorden;
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 Ze voeden u op tot heilzame tucht, Rechtschapenheid, plichtsbesef en oprechtheid.
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 Aan de onnozelen schenken ze ervaring, Aan jonge mensen doordachte kennis.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 Als een wijze ze hoort, zal hij zijn inzicht verdiepen, Een verstandig mens zal er ideeën door krijgen;
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 Spreuk en strikvraag zal hij doorzien, De woorden der wijzen en hun problemen.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 Het ontzag voor Jahweh is de grondslag der wijsheid; Maar ongelovigen lachen om wijsheid en tucht.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Mijn zoon, luister dus naar de wenken van uw vader, Sla niet in de wind, wat uw moeder u leerde;
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 Want het siert uw hoofd als een krans, Uw hals als een snoer.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Mijn zoon, als zondaars u willen verleiden, stem niet toe,
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 Als ze u zeggen: Ga met ons mee, Laat ons loeren op bloed, Laat ons zo maar onschuldigen belagen,
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 Gelijk de onderwereld hen levend verslinden, Als zij, die ten grave dalen, geheel en al; (Sheol )
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
13 Allerlei kostbare schatten zullen we vinden, Onze huizen vullen met buit;
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Ge moogt meeloten in onze kring, Eén buidel zullen we samen delen!
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 Mijn zoon, ga dan niet met hen mee, En houd uw voet af van hun pad;
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 Want hun voeten ijlen naar het kwade, En haasten zich, om bloed te vergieten.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Maar zoals het niet geeft, of het net wordt gespannen, Terwijl alle vogels het zien:
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 Zo loeren ze slechts op hun eigen bloed, En belagen ze hun eigen leven!
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Zo gaat het allen, die uit zijn op oneerlijke winst: Deze beneemt zijn bezitters het leven.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 De wijsheid roept luid in de straten, Op de pleinen verheft ze haar stem;
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 Ze roept op de tinne der muren, En spreekt aan de ingang der poorten:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 Hoe lang nog, dommen, blijft gij liever onnozel, Blijven de eigenwijzen verwaand, Willen de dwazen van geen wijsheid horen?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Keert u tot mijn vermaning; Dan stort ik mijn geest over u uit, En maak u mijn woorden bekend.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Maar zo ge weigert, als ik roep, En niemand er op let, als ik mijn hand verhef;
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 Zo ge mijn raad geheel en al in de wind slaat, En van mijn vermaning niet wilt weten:
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 Zal ik lachen, wanneer het u slecht gaat, Zal ik spotten, wanneer uw verschrikking komt als een onweer;
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 Wanneer uw ongeluk nadert als een orkaan, Wanneer benauwdheid en angst u overvallen!
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Dan zal men mij roepen, maar zal ik niet antwoorden, Zal men mij zoeken, maar mij niet vinden!
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Omdat ze van wijsheid niets wilden weten, En het ontzag voor Jahweh niet hebben verkozen,
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 Van mijn raad niets moesten hebben, En al mijn vermaan in de wind hebben geslagen:
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Zullen ze eten de vrucht van hun wandel, Verzadigd worden met wat ze beraamden.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 Want de onnozelen komen door hun onverschilligheid om, De dwazen storten door hun lichtzinnigheid in het verderf;
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 Maar die naar mij luistert, zal in veiligheid wonen, Bevrijd van de vrees voor de rampen!
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”