< Spreuken 3 >
1 Mijn zoon, vergeet mijn onderricht niet, Neem mijn wenken ter harte.
Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
2 Ze schenken u lengte van dagen, jaren van leven, En overvloedige welvaart!
gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
3 Liefde en trouw mogen u nimmer verlaten, Hang ze om uw hals, schrijf ze op de tafel van uw hart;
Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Dan zult ge goed en verstandig zijn, In de ogen van God en de mensen.
Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
5 Vertrouw op Jahweh met heel uw hart, Verlaat u niet op uw eigen inzicht;
Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
6 Denk aan Hem op al uw wegen, Dan zal Hij uw paden effenen.
cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
7 Wees niet wijs in uw eigen ogen, Heb ontzag voor Jahweh en vermijd het kwaad:
Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
8 Het zal genezing brengen voor uw lichaam, Verkwikking voor uw gebeente.
Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
9 Eer Jahweh met heel uw bezit, Met het beste van al uw inkomsten:
Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
10 Dan zullen uw schuren vol koren zijn, Uw kuipen bersten van most.
ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
11 Mijn zoon, sla de lessen van Jahweh niet in de wind, Heb geen afkeer van zijn bestraffing;
Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
12 Want Jahweh tuchtigt hem, dien Hij liefheeft, Kastijdt het kind, dat Hij mag.
domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
13 Gelukkig de mens, die wijsheid verkreeg, De man die inzicht bekwam;
Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
14 Want haar voordelen zijn groter dan die van zilver, Wat zij opbrengt is beter dan goud.
gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
15 Zij is meer waard dan juwelen; Geen van uw kostbaarheden komt haar nabij!
Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
16 Met de rechterhand schenkt ze lengte van dagen, Met de linker rijkdom en aanzien.
Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
17 Haar wegen zijn liefelijke wegen, Al haar paden leiden tot vrede;
Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
18 Zij is een boom des levens voor wie haar vatten, En wie haar vasthoudt, is zalig te prijzen!
Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
19 Met wijsheid heeft Jahweh de aarde gegrond, Met inzicht de hemel gewelfd;
Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
20 Naar zijn kennis rollen de zeeën aan, En druppelen de wolken van dauw.
ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
21 Mijn zoon, verlies ze dus niet uit het oog, Maar doe alles met beleid en verstand;
Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
22 Laat ze het leven zijn voor uw ziel, Een sieraad voor uw hals.
za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
23 Dan zult ge veilig uw weg bewandelen, En zult ge uw voeten niet stoten;
Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
24 Dan behoeft ge niet te vrezen, als ge u neerlegt, Kunt ge rustig sluimeren, als ge wilt slapen.
sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
25 Dan behoeft ge niet te vrezen, voor wat de dommen verschrikt, Of als het onweer komt, dat de bozen overvalt;
Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
26 Want Jahweh zal zijn op al uw wegen, Uw voet behoeden voor de strik.
gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
27 Weiger het goede niet, aan wien het toekomt, Zolang het in uw macht is, het te doen.
Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
28 Zeg niet tot uw naaste: "Ga heen en kom nog eens terug"; Of "Mórgen krijgt ge iets", terwijl ge het nú hebt!
Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
29 Smeed geen kwaad tegen uw naaste, Terwijl hij, niets duchtend, bij u verblijft;
Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
30 Zoek geen twist met iemand om niets, Als hij u geen kwaad heeft gedaan.
Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
31 Wees niet jaloers op een tyran, Laat geen zijner wegen u gevallen;
Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
32 Want Jahweh heeft een afschuw van den zondaar, Maar met de rechtvaardigen gaat Hij vertrouwelijk om.
Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
33 De vloek van Jahweh rust op het huis van den boze, Zijn zegen op de woning der rechtvaardigen;
La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
34 Met spotters drijft Hij de spot, Maar aan de nederigen schenkt hij genade.
Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
35 Wijzen zullen achting verwerven, Dwazen schande verkrijgen!
Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.