< Klaagliederen 3 >
1 Ik ben de man, die ellende aanschouwde Door de roede van zijn verbolgenheid;
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Hij heeft mij gedreven en opgejaagd De diepste duisternis in;
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Telkens keerde Hij zijn hand tegen mij, Elke dag opnieuw.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Hij heeft mijn vlees en huid doen verkwijnen, Mijn beenderen gebroken;
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 Overal rond mij opgestapeld Gal en kommer;
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 Mij in het donker doen zitten Als de doden uit aloude tijden.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Hij metselde mij in, zodat ik niet kon ontsnappen, En verzwaarde mijn ketens;
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Hoe ik ook klaagde en schreide, Hij bleef doof voor mijn smeken;
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Hij versperde mijn wegen met stenen, Vernielde mijn paden.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Hij loerde op mij als een beer, Als een leeuw, die in hinderlaag ligt;
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 Hij sleurde mij van mijn wegen, om mij te verscheuren, En stortte mij in het verderf;
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 Hij spande zijn boog, En maakte mij doel van de pijl.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Hij schoot door mijn nieren De pijlen van zijn koker.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Voor alle volken werd ik een hoon, Een spotlied altijd herhaald.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Hij heeft met bitterheid mij verzadigd, Met alsem gedrenkt.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 Op kiezel heeft Hij mijn tanden doen bijten, Met as mij gespijsd;
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 De vrede werd mijn ziel ontroofd, Wat geluk is, ken ik niet meer.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 Ik zeide: Weg is mijn roemen, Mijn hopen op Jahweh!
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Gedenk toch mijn nood en mijn angst, Mijn alsem en gal!
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Ja, Gij zult zeker gedenken, Hoe mijn ziel gaat gebukt:
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Dit blijf ik altijd bepeinzen, Hierop altijd vertrouwen!
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Neen, Jahweh’s genaden nemen geen einde, Nooit houdt zijn barmhartigheid op:
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 Iedere morgen zijn ze nieuw, En groot is uw trouw.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 Mijn deel is Jahweh! zegt mijn ziel, En daarom vertrouw ik op Hem!
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Goed is Jahweh voor die op Hem hopen, Voor iedereen, die Hem zoekt;
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 Goed is het, gelaten te wachten Op redding van Jahweh;
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Goed is het den mens, zijn juk te dragen Van de prilste jeugd af!
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Hij moet in de eenzaamheid zwijgen, Wanneer Hij het hem oplegt;
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Zijn mond in het stof blijven drukken. Misschien is er hoop;
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Zijn wangen bieden aan hem, die hem slaat, Verzadigd worden met smaad.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Neen, de Heer verlaat niet voor immer De kinderen der mensen!
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Neen, na de kastijding erbarmt Hij zich weer, Naar zijn grote ontferming:
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Want niet van harte plaagt en bedroeft Hij De kinderen der mensen!
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Dat men onder de voeten treedt, Allen, die in het land zijn gevangen:
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 Dat men het recht van een ander verkracht Voor het aanschijn van den Allerhoogste:
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 Dat men den naaste geen recht laat geschieden: Zou de Heer dat niet zien?
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Neen, op wiens bevel het ook is geschied, Heeft de Heer het niet geboden?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Komt niet uit de mond van den Allerhoogste Het kwaad en het goed?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Wat klaagt dan de mens bij zijn leven: Laat iedereen klagen over zijn zonde!
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Laten wij ons gedrag onderzoeken en toetsen, En ons tot Jahweh bekeren;
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Heffen wij ons hart op de handen omhoog Tot God in de hemel!
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 Wij bleven zondigen, en waren opstandig: Gij kondt geen vergiffenis schenken!
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Toen hebt Gij in toorn u gepantserd en ons achtervolgd, Meedogenloos ons gedood;
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 U gehuld in een wolk, Waar geen bidden doorheen kon;
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Tot vuil en uitschot ons gemaakt Te midden der volken.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Nu sperren allen de mond tegen ons op, Die onze vijanden zijn;
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Nu liggen wij in schrik en strik, Verwoesting, vernieling;
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Nu storten onze ogen beken van tranen Om de ondergang van de dochter van mijn volk.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Rusteloos stromen mijn ogen En zonder verpozing,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Totdat Jahweh neerblikt, Uit de hemel toeziet.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Mijn oog doet mij wee Van al het schreien over mijn stad.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Als een vogel maakten ze jacht op mij, Die zonder reden mijn vijanden zijn;
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 Zij smoorden mij levend in een put, En wierpen mij nog stenen na;
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Het water stroomde over mijn hoofd, Ik dacht: Nu ben ik verloren!
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Toen riep ik uw Naam aan, o Jahweh, Uit het diepst van de put!
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Gij hebt mijn smeken gehoord, uw oor niet gesloten Voor mijn zuchten en schreien;
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Gij zijt gekomen, toen ik U riep, En hebt gesproken: Wees niet bang!
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Heer, Gij naamt het voor mij op, En hebt mijn leven gered!
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Jahweh, Gij hebt mijn verdrukking gezien, Mij recht verschaft;
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Gij hebt hun wraakzucht aanschouwd, Al hun plannen tegen mij.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Jahweh, Gij hebt hun spotten gehoord, Al hun plannen tegen mij.
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 Mijn vijand heeft lippen zowel als gedachten Altijd tegen mij gericht.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Zie toe; want of ze zitten of staan, Een spotlied ben ik voor hen!
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Jahweh, vergeld ze hun daden, Het werk hunner handen!
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Sla hun hart met verblinding, Henzelf met uw vloek;
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Vervolg en verniel ze in gramschap Onder uw hemel, o Jahweh!
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.