< Job 6 >

1 Job antwoordde, en sprak:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Ach, mocht mijn wrevel worden gewogen, Maar tegelijk met mijn leed op de weegschaal gelegd:
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3 Want omdat het zwaarder is dan het zand aan de zee, Daarom gingen ook mijn woorden de perken te buiten.
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4 Ja, de pijlen van den Almachtige blijven in mij steken, Mijn geest zuigt er het gif van op; De verschrikkingen Gods Stellen zich tegen mij in slagorde op!
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.
5 Balkt soms de woudezel bij het gras Of loeit het rund bij zijn kribbe?
Jaki yakan yi kuka sa’ad da ya sami ciyawar ci, ko saniya takan yi kuka in ta sami abincinta?
6 Kan het laffe zonder zout worden gegeten, Of is er smaak aan het wit van een ei?
Akan cin abinci marar ɗanɗano ba tare da an sa gishiri ba, ko akwai wani ƙanshin daɗi a cikin farin ruwan ƙwai?
7 Neen, ik weiger, het aan te raken, Ze zijn voor mij een walgelijke spijs!
Na ƙi in taɓa shi; irin wannan abinci zai sa ni rashin lafiya.
8 Ach, dat mijn bede werd verhoord, En dat God mijn wens mocht vervullen;
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9 Dat het God behaagde, mij te verpletteren, Zijn hand zich bewoog, om mij weg te maaien.
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10 Dat zou een troost voor mij zijn, En ik danste ondanks mijn leed: "Hij spaart mij niet, Omdat ik den Heilige mijn wens niet verzweeg!".
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11 Want wat is mijn kracht, dat ik nu nog zou wachten, Wat mijn uitzicht, dat ik langer zou leven?
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12 Is mijn kracht soms als die van een steen, Is mijn vlees soms van brons?
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13 Ben ik niet geheel van redding verstoken, Is iedere hulp mij niet ontzegd?
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
14 Maar wie zijn vriend barmhartigheid weigert, Verzaakt de vrees voor den Almachtige!
“Duk wanda ya ƙi yă yi alheri ga aboki ya rabu ta tsoron Maɗaukaki.
15 Toch zijn mijn broeders als een beek onbetrouwbaar, Als een stortbeek, die wegstroomt:
Amma’yan’uwana sun nuna ba zan iya dogara gare su ba, kamar rafin da yakan bushe da rani,
16 Die bedekt zijn met ijs, Of bedolven onder sneeuw;
kamar rafin da yakan cika a lokacin ƙanƙara, yă kuma kumbura kamar ƙanƙarar da ta narke,
17 Zodra de hitte komt, drogen zij uit, Zodra het warm wordt, zijn ze verdwenen.
amma da rani sai yă bushe, lokacin zafi ba a samun ruwa yana gudu a wurin.
18 Ze buigen af van de weg, die ze gaan, En verliezen zich in de woestijn;
Ayari sukan bar hanyarsu; sukan yi ta neman wurin da za su sami ruwa, su kāsa samu har su mutu.
19 De karavanen van Tema zien er naar uit, De convooien van Sjeba hebben er hun hoop op gevestigd:
Ayarin Tema sun nemi ruwa, matafiya’yan kasuwa Sheba sun nema cike da begen samu.
20 Maar ze worden in hun verwachting beschaamd, Staan bij hun aankomst te schande.
Ransu ya ɓace, domin sun sa zuciya sosai; sa’ad da suka kai wurin kuwa ba su sami abin da suka sa zuciyar samu ba.
21 Zo zijt gij voor mij nu geworden: Gij aanschouwt mijn ellende, en beangst deinst gij terug!
Yanzu kuma kun nuna mini ba ku iya taimako; kun ga abin bantsoro kuka tsorata.
22 Heb ik gevraagd: Geeft mij iets ten geschenke, Of staat mij van uw vermogen iets af;
Ko na taɓa cewa, ‘Ku ba da wani abu a madadina, ko na roƙe ku, ku ba da wani abu domina daga cikin dukiyarku,
23 Of redt mij uit de hand van den vijand, Bevrijdt mij uit de greep der tyrannen?
ko kuma kun taɓa kuɓutar da ni daga hannun maƙiyina, ko kun taɓa ƙwato ni daga hannun marasa kirki’?
24 Neen, onderricht mij, en dan zal ik zwijgen; Laat mij inzien, waarin ik heb gedwaald!
“Ku koya mini, zan yi shiru; ku nuna mini inda ban yi daidai ba.
25 Hoe zoet zijn woorden, die oprecht zijn gemeend, Maar hoe grievend de berisping van u!
Faɗar gaskiya tana da zafi! Amma ina amfanin gardamar da kuke yi?
26 Meent gij, mijn woorden te moeten berispen: Woorden van een wanhopige, die in de wind zijn gesproken?
Ko kuna so ku gyara abin da na faɗi ne, ku mai da magana wanda yake cikin wahala ta zama ta wofi?
27 Wilt gij het lot over een onschuldige werpen, En de staf breken over uw vriend?
Kukan yi ƙuri’a a kan marayu ku kuma sayar da abokinku.
28 Welnu dan, wilt mij aanhoren: Ik lieg u toch niet in het gezicht.
“Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
29 Bezint u, en laat er geen onrecht geschieden; Bezint u, mijn onschuld zal blijken!
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
30 Is er soms onrecht op mijn tong, Of kan mijn gehemelte de rampen niet proeven;
Ko akwai wata mugunta a bakina? Bakina ba zai iya rarrabewa tsakanin gaskiya da ƙarya ba?

< Job 6 >