< Job 38 >
1 Nu nam Jahweh het woord, en sprak tot Job in de storm:
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2 Wie zijt gij, die de Voorzienigheid duister maakt Door woorden zonder verstand?
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3 Omgord uw lenden als een man, Ik zal u vragen stellen, gij moogt Mij leren!
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4 Waar waart ge, toen Ik de aarde grondde: Vertel het, zo ge er iets van weet!
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5 Wie heeft haar grootte bepaald: gij weet het zo goed; Wie het meetsnoer over haar gespannen?
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6 Waarop zijn haar zuilen geplaatst, Of wie heeft haar hoeksteen gelegd:
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7 Onder het gejuich van het koor der morgensterren, Het jubelen van de zonen Gods?
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8 Wie heeft de zee achter deuren gesloten, Toen zij bruisend uit de moederschoot kwam;
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9 Toen Ik haar de wolken gaf als een kleed, De nevel als haar windsels;
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10 Toen Ik haar grenzen heb gesteld, Slagboom en grendels haar gaf;
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11 Toen Ik sprak: Ge komt tot hier en niet verder, Hier wordt de trots van uw golven gebroken!
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12 Hebt gij ooit in uw leven de morgen ontboden, De dageraad zijn plaats bestemd,
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13 Om de zomen der aarde te bezetten En er vlammen uit te schudden?
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14 Zij flonkert als een kostbare zegelsteen, Wordt bontgeverfd als een kleed,
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15 Totdat de stralen hun licht wordt ontnomen, Hun opgeheven arm wordt gebroken.
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16 Zijt ge doorgedrongen tot de bronnen der zee, Hebt ge de bodem van de Oceaan bewandeld;
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17 Zijn u de poorten des doods getoond, De wachters der duisternis u verschenen;
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18 Hebt ge de breedten der aarde omvat: Zeg op, wanneer ge dit allemaal weet!
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
19 Waar is de weg naar de woning van het licht, En waar heeft de duisternis haar verblijf,
“Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
20 Zodat gij ze naar hun plaats kunt brengen, En hun de paden naar huis kunt leren?
Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
21 Ge weet het toch, want toen werdt ge geboren, Het getal van uw jaren is immers zo groot!
Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
22 Zijt ge doorgedrongen tot de schuren der sneeuw, Hebt ge de opslagplaatsen van de hagel aanschouwd,
“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
23 Die Ik heb opgespaard voor de tijd van benauwing, Voor de dag van aanval en strijd?
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
24 Waar is de weg, waar de kou zich verspreidt, Waar de oostenwind over de aarde giert?
Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
25 Wie heeft voor de stortvloed kanalen gegraven, En paden voor de donderwolken,
Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
26 Om regen te geven op onbewoond land, Op steppen, waar zich geen mens bevindt;
don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
27 Om woestijn en wildernis te verzadigen, Uit de dorre grond het gras te doen spruiten?
don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
28 Heeft de regen een vader, Of wie heeft de druppels van de dauw verwekt;
Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
29 Uit wiens schoot is het ijs te voorschijn gekomen, Wie heeft het rijp in de lucht gebaard?
Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
30 De wateren worden hard als steen, De vlakte van de Afgrond sluit zich aaneen!
lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
31 Kunt gij de banden der Plejaden knopen, Of de boeien van de Orion slaken;
“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
32 Kunt gij de maan op tijd naar buiten doen treden, Leidt gij de Beer met zijn jongen?
Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
33 Schrijft gij de hemel de wetten voor, Stelt gij zijn macht over de aarde vast;
Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
34 Verheft gij uw stem tot de wolken, Gehoorzaamt ù de watervloed?
“Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
35 Zendt gij de bliksems uit, en ze gaan; Zeggen ze tot u: Hier zijn we terug?
Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
36 Wie heeft inzicht aan den reiger gegeven Verstand geschonken aan den haan;
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37 Wie telt met wijsheid de wolken af, En giet de zakken van de hemel leeg:
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38 Wanneer de bodem hard is als ijzer, De kluiten aan elkander kleven?
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39 Jaagt gij een prooi voor de leeuwin, Stilt gij de honger der welpen,
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40 Wanneer ze in hun holen liggen, Of loeren tussen de struiken?
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41 Wie geeft ze tegen de avond haar buit, Wanneer haar jongen tot de Godheid roepen, En zonder voedsel rond blijven snuffelen, Op zoek naar spijs?
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?