< Job 21 >

1 Job antwoordde, en sprak:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Luistert aandachtig naar wat ik ga zeggen; En dat uw troost zich daartoe bepale!
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Laat mij uitspreken op mijn beurt, Wanneer ik klaar ben, kunt ge spotten!
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Heb ik me soms over mensen beklaagd, Of heb ik geen grond, om mismoedig te zijn?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Ziet mij aan, en staat verstomd, En legt uw hand op de mond!
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Wanneer ik er aan denk, sta ik verbijsterd, En huivert mijn vlees:
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 "Waarom blijven de bozen in leven Worden zij oud en groeien in kracht?"
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Hun kroost gedijt voor hun aanschijn, Hun geslacht houdt stand voor hun ogen;
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Hun huizen zijn veilig en zonder vrees, Gods roede valt er niet op neer.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Hun stier bespringt en bevrucht, Hun koeien kalven en hebben geen misdracht;
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Als een kudde laten ze hun jongens naar buiten, En hun kinderen springen rond.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 Ze zingen bij pauken en citer, Vermaken zich bij de tonen der fluit;
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Ze slijten hun dagen in weelde, En dalen in vrede ten grave. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 Toch zeggen ze tot God: Blijf verre van ons, We willen uw wegen niet kennen!
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Wat is de Almachtige, dat we Hem zouden dienen; Wat baat het ons, te smeken tot Hem?
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Ligt hun geluk niet in hun eigen hand, Bemoeit Hij Zich wel met de plannen der bozen?
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Hoe dikwijls gaat de lamp der bozen wel uit, En stort er rampspoed op hen neer? Hoe dikwijls vernielt Hij de slechten in zijn toorn, Grijpen de weeën hen aan in zijn gramschap;
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 Worden zij als stro voor de wind, Als kaf, opgejaagd door de storm?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 Gij zegt: God wreekt zijn misdaad op zijn kinderen, En zal hem zo zijn wraak laten voelen!
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Maar zijn eigen ogen moesten zijn rampspoed aanschouwen, Zelf moest hij de toorn van den Almachtige drinken!
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Want wat bekommert hij zich om zijn gezin na zijn dood, Wanneer het getal zijner maanden ten einde is?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Zou men soms God de les willen lezen, Hij, die de hemelingen richt?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 En de een gaat dood, geheel voldaan, Volkomen gelukkig en rustig,
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 Zijn lenden vol vet, Het merg in zijn beenderen nog fris.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 De ander sterft met een verbitterd gemoed, Zonder ooit het geluk te hebben gesmaakt!
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Tezamen liggen ze neer in het stof, Door de wormen bedekt!
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Zeker, ik ken uw gedachten, En de bedenkingen, die gij tegen mij aanvoert;
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 Gij zegt: "Waar is het huis van den tyran, Waar de tent, waar de bozen in wonen?"
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Hebt gij de reizigers dan nooit ondervraagd, Of aanvaardt gij hun getuigenis niet:
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 "De boze blijft gespaard op de dag van verderf, En ontsnapt op de dag van de gramschap!"
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Wie houdt hem zijn wandel voor ogen, Wie zet hem betaald wat hij deed?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Hij wordt ten grave gedragen, En een tombe houdt er de wacht.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Zacht ligt hij neer Op de kluiten in het dal; Heel de wereld trekt achter hem aan, Talloos velen lopen uit voor zijn stoet.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Wat is uw vertroosting dus schraal, Uw antwoord anders dan leugens!
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >