< Job 20 >

1 Daarop nam Sofar van Naäma het woord en sprak:
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Mijn inzicht dwingt mij tot antwoord, Omdat het in mij stormt,
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 Nu ik een grievend verwijt moet horen, En domme bluf mij antwoord geeft.
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 Weet ge dan niet, dat van de vroegste tijd af, Sinds de mens op de aarde werd geplaatst,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 Het gejuich van den boze slechts korte tijd duurt, De vreugde van den goddeloze een ogenblik?
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Al verheft zijn gestalte zich hemelhoog, En reikt zijn hoofd tot de wolken:
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 Als zijn eigen drek verdwijnt hij voor immer, Die hem zagen, roepen: Waar is hij?
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 Spoorloos vervluchtigt hij als een droom, Wordt weggevaagd als een nachtgezicht;
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 Het oog, dat hem zag, bespeurt hem niet langer, De plaats, waar hij woonde, aanschouwt hem niet meer.
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 Zijn zonen bedelen bij armen, Zijn kinderen geven zijn rijkdom af;
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 En al is zijn gebeente vol jeugdige kracht, Het legt zich neer bij hem in het graf.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 Hoe zoet het slechte in zijn mond mag smaken, Hoe hij het onder zijn tong ook verbergt,
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 Hoe hij het smekt en niet doorslikt, En het tegen zijn gehemelte houdt:
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 Toch verschaalt zijn spijs in zijn ingewanden, Wordt in zijn binnenste adderengif;
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 Hij slokt schatten in, maar braakt ze uit, God drijft ze weer uit zijn buik.
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 Adderengif moet hij drinken, Een slangentong zal hem doden;
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 Hij zal geen beken van olie genieten, Geen stromen van honing en boter.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 Zijn winst geeft hij terug, en slokt ze niet door, Verheugt zich niet in de vrucht van zijn handel;
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 Want hij heeft de armen verdrukt en verlaten, Hun huis geroofd, niet gebouwd.
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 Omdat hij voor zijn buik geen verzadiging vond, Niets aan zijn eetlust ontsnapte,
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 En niets aan zijn vraatzucht ontging: Daarom houdt zijn voorspoed geen stand!
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 Op het toppunt van zijn geluk wordt het hem bang, Wordt hij door al de slagen van rampspoed getroffen;
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 Terwijl hij zijn buik vult, laat God zijn ziedende toorn op hem los, Laat schichten regenen op zijn ingewanden.
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 Als hij vlucht voor de ijzeren wapenrusting, Doorboort hem de koperen boog,
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 Puilt de schicht uit zijn rug, De bliksemende pijl uit zijn gal. Dan overvalt hem de doodschrik,
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 De diepste duisternis houdt hem omvangen; Een vuur verslindt hem, dat niet is ontstoken, Vreet weg wat nog leeft in zijn tent.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 De hemelen openbaren zijn schuld, En de aarde staat tegen hem op;
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 Een stortvloed spoelt zijn woning weg, Een vloedgolf op de dag van zijn toorn!
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 Dit is het lot van den boze, door God hem bedeeld, Het erfdeel, dat de Godheid hem toewijst!
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”

< Job 20 >