< Job 16 >
1 Job antwoordde, en sprak:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Zulke beweringen heb ik nu al meer dan genoeg gehoord; Gij zijt allemaal onuitstaanbare troosters!
“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
3 Komt er dan nooit een eind aan die bluf, Wat prikkelt u toch, om te praten?
Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
4 Ik zou juist eender als gij kunnen spreken, Waart gij in mijn plaats; Mooie woorden tegen u kunnen zeggen, Het hoofd over u kunnen schudden;
Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
5 U met de mond kunnen troosten, En met de lippen beklagen.
Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
6 Als ik spreek, wordt mijn leed er niet door verminderd; Maar wat komt er van mij, als ik zwijg?
“Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
7 De kwaadwillige zou mij aanstonds weerloos maken En heel zijn bent greep mij aan;
Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
8 Mijn lasteraar zou tegen mij getuigen, Tegen mij optreden, mij aanklagen;
Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
9 Zijn toorn verscheurt en bestookt mij, Hij knerst de tanden tegen mij! Mijn tegenstanders zouden mij met hun ogen doorboren,
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
10 Hun monden tegen mij opensperren, Smadelijk mij op de wangen slaan, Als één man tegen mij optrekken!
Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
11 Want God levert mij aan deugnieten over, En werpt mij in de handen der bozen;
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
12 Ik leefde in vrede: Hij heeft me gebroken, Bij de nek gegrepen en neergesmakt; Hij heeft mij tot zijn doelwit gemaakt,
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
13 Zijn pijlen snorren om mij heen; Meedogenloos doorboort Hij mijn nieren, En stort mijn gal over de bodem uit.
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
14 Hij schiet mij de ene bres na de andere, Als een krijgsheld stormt Hij op mij los;
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
15 Ik heb een rouwkleed over mijn huid genaaid, Mijn hoorn in het stof laten zakken;
“Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
16 Mijn gelaat is rood van het wenen, En over mijn wimpers ligt de schaduw des doods.
Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
17 Maar omdat er geen geweld aan mijn handen kleeft, Klinkt mijn rein gebed naar omhoog:
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
18 Aarde, houd mijn bloed niet bedekt En smoor mijn jammerklacht niet!
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
19 Maar nog leeft mijn Getuige in de hemel, Mijn pleitbezorger in den hoge!
Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
20 Mijn jammeren dringt door tot God, Mijn oog stort tranen voor zijn aanschijn.
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
21 O, mocht er een scheidsrechter zijn tussen den mens en God, Als tussen den mens en zijn naaste!
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
22 Want luttel zijn de jaren, die mij nog resten, Eer ik de weg bewandel, waarlangs men niet terugkeert.
“Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.