< Zaburi 67 >
1 Kuom jatend wer. Gik miwergo man-gi tondegi. Zaburi. Wer. Mad Nyasaye timnwa ngʼwono kendo owinjwa; mad omi wangʼe rienynwa maber, (Sela)
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Tare da kayan kiɗi masu tsirkiya. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă yi mana alheri yă kuma albarkace mu yă kuma sa fuskarsa ta haskaka a kanmu, (Sela)
2 mondo yoreni ongʼere e piny, kendo ogendini duto oyud warruokne.
don a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma a cikin dukan al’ummai.
3 Mad ji paki, yaye Nyasaye; mad ji duto opaki.
Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe ka.
4 Mad ogendini obed mamor kendo ower gi ilo, nikech irito ji gi ratiro, kendo itayo ogendini mag piny. (Sela)
Bari al’ummai su yi murna su kuma rera don farin ciki, gama kana mulkin mutanenka da adalci kana kuma bi da al’umman duniya. (Sela)
5 Mad ji paki, yaye Nyasaye; mad ji duto opaki.
Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe.
6 Eka piny biro chiego cham kaka owinjore kendo Nyasaye, ma Nyasachwa, biro gwedhowa.
Sa’an nan ƙasa za tă ba da girbinta Allah kuma, Allahnmu, zai albarkace mu.
7 Nyasaye biro gwedhowa, kendo piny duto koni gi koni biro luore.
Allah yă sa mana albarka, dukan iyakar duniya kuma su ji tsoronsa.