< Jongʼad Bura 16 >

1 Chiengʼ moro achiel Samson nodhi Gaza, kama nonenoe nyako moro ma jachode mi odhi mondo oterre kode.
Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
2 Nonyis jo-Gaza niya, “Samson nitiere kae!” Omiyo negilworo kanyo kendo gibuto ka girite otieno duto e dhoranga dala maduongʼ. Ne ok gisudo otienono, kagiwacho niya, “Kochopo kogwen to wabiro nege.”
Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
3 To Samson nonindo kanyo nyaka dier otieno. Eka no-aa malo kendo nomako ranga dalano kaachiel gi sirnine ariyo mopudhogi kod gik moko duto. Notingʼogi e goke mi oterogi ewi got momanyore gi Hebron.
Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
4 Bangʼ mano, nomako osiep hera gi nyako ma nyinge Delila e Holo mar Sorek.
Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
5 Jotend jo-Filistia nodhi ir Delila mi owachone niya, “Tem ane ka inyalo hoye mondo onyisi kuma tekone ae kendo ingʼe kaka wanyalo loye mondo mi watweye kendo sande. Wabiro miyi fedha ma pekne romo kilo apar gadek ngʼato ka ngʼato.”
Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
6 Omiyo Delila nowachone Samson niya, “Nyisa ane kuma tekoni ae kendo kaka inyalo maki mi tweyi.”
Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
7 Samson nodwoke niya, “Ka ngʼato otweya gi tonde abiriyo manyien mapok otiyo, to abiro bedo manyap machal gi ngʼato angʼata.”
Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
8 Eka jotelo mag jo-Filistia nokelone Delila tonde abiriyo manyien mapok otiyo, eka notweye gi tondego.
Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
9 Kane osepando jomoko ei ot kanyo, noluonge kowacho niya, “Samson, jo-Filistia osebiro monji!” To ne ochodo tondego e yo mayot mana kaka tol chot kokete machiegni gi mach. Omiyo kuma tekone ae ne ok ofweny.
Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
10 Eka Delila nowachone Samson niya, “Isekawa ngʼama ofuwo; ne iwuonda. Bi mondo koro inyisa kaka inyalo tweyi.”
Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
11 Nowachone niya, “Ka ngʼato otweya moridore gi tonde manyien mapok otiyo, to abiro bedo manyap machal gi ngʼato angʼata.”
Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
12 Omiyo Delila nokawo tonde manyien mi otweyego. Kane osepando jomoko ei ot kanyo, noluonge kowacho niya, “Samson, jo-Filistia osebiro monji!” To nochodo tondego mana ka gima gin usi.
Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
13 Eka Delila nowachone Samson niya, “Nyaka sani, isebedo ka ikawa ka ngʼama ofuwo kendo isewuonda. Nyisa kaka inyalo tweyi.” Nodwoko niya, “Ka ikado yie wiya gi usi mar chwecho kendo miride gi pino, to anabed manyap machal gi ngʼato angʼata.” Omiyo kane onindo Delila nokado yie wiye nyadibiriyo, kotwangʼe matek gi usi mar chwecho
Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
14 kendo oride motegno gi pino. Noluonge kendo niya, “Samson, jo-Filistia osebiro monji.” Nochiewo oa e nindo mi opudho pino oko kod usi mar chwecho.
ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
15 Bangʼe nowachone niya, “Ere kaka inyalo wacho ni ihera to ok inyal nyisa kuma tekoni ae? Ma koro en mar adek ma iseketa ka ngʼama ofuwo kendo pod ok inyisa kuma tekoni ae.”
Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
16 Noromo Samson gi wachni pile ka pile manomiyo koro odwaro mana dere.
Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
17 Omiyo nohulone gik moko duto kowachone niya, “Onge wembe mosekadho e wiya nikech asebedo ja-Nazir ma Nyasaye nowalo nyaka aa nywolna. Ka yie wiya oliel, to tekra biro rumo, kendo abiro bedo manyap machal gi ngʼato angʼata.”
Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
18 Ka Delila noneno nine osenyise gik moko duto, nooro wach ne jotend jo-Filistia niya, “Dwoguru dichiel; osenyisa gik moko duto.” Omiyo jotend jo-Filistia noduogo gi chudo e lwetgi.
Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
19 Delila nohoyo Samson mi nonindo koteno wiye kuome, eka noluongo ngʼato mondo obi oliel yie wiye mane osekad nyadibiriyo. Bangʼ mano tekre norumo.
Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
20 Eka noluonge niya, “Samson, jo-Filistia osebiro mondo omonji!” Kane ochiewo to ne owacho e chunye niya, “Abiro wuok kaka pile mondo abed thuolo.” To ne ok ongʼeyo ni Jehova Nyasaye noseweye.
Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
21 Bangʼe jo-Filistia nomake, mi gilodho wengene oko kendo ne gitere nyaka Gaza. Eka ne gitweye gi nyoroche mag mula, mi gikete jarego e od twech.
Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
22 To bangʼe yie wiye nochako twi mos mos.
Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
23 Koro jotend jo-Filistia nochokore mondo gitim misango maduongʼ ne Dagon ma nyasachgi, negitimo nyasi kagiwacho niya, “Nyasachwa osechiwo Samson ma jasikwa e lwetwa.”
To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
24 Ka ji nonene, negipako nyasachgi, kagiwacho niya, “Nyasachwa osechiwo jasikwa e lwetwa, ngʼatno mane oketho pinywa mi omiyo onegwa mangʼeny.”
Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
25 E seche mane gin-gi ilo mathothno, negigoyo koko niya, “Keluru Samson mondo omielnwa.” Omiyo negigolo Samson oko mar od twech, mi omielnegi. Kane oyudo gichunge e kind sirni,
Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
26 Samson nowachone jatich mane omako lwete niya, “Keta ane kama anyalo muloe sirni mosiro hekaluni, mondo omi ayiengra kuomgi.”
sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
27 Koro hekalu nopongʼ gi chwo kod mon; jotend jo-Filistia duto ne ni kanyo, kendo ne nitie chwo gi mon alufu adek mane ni ewi tado ka ngʼiyo Samson kamiel.
To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
28 Eka Samson noywak ne Jehova Nyasaye niya, “Yaye Jehova Nyasaye Manyalo Gik Moko Duto, para! Yaye Nyasaye, duogna teko mana dichiel kende mondo achulgo kuor kuom jo-Filistia-gi kuom toko wengena ariyo oko.”
Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
29 Eka Samson nomako sirni ariyo mane ni e chuny hekalu mane osiro hekalu. Kosirogi moro ka moro, ka lwedo korachwich osiro achiel to lwedo koracham e machielo,
Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
30 Samson nowacho niya, “Mad iyie atho gi jo-Filistia-gi!” Eka nodhiro sirnigo gi tekone duto, kendo hekalu norwombore piny kuom jotelo kod ji duto mane ni e iye. Omiyo nonego ji mangʼeny sa ma notho moloyo kane ongima.
Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
31 Eka owetene kod joka wuon mare duto nodhi mondo okawe. Negikele ma gi hike e kind Zora gi Eshtaol e liend Manoa wuon mare. Notelo ne Israel kuom higni piero ariyo.
Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.

< Jongʼad Bura 16 >