< Jeremia 33 >

1 Kane pod Jeremia oketi e agola kamane irite, wach Jehova Nyasaye nobirone mar ariyo ni:
Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
2 “Ma e gima Jehova Nyasaye wacho, en ema nochweyo piny, Jehova Nyasaye mane olose kendo oketo mise mare, Jehova Nyasaye e nyinge:
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
3 ‘Bi ira, kendo anaduoki, kendo ananyisi gik madongo ma ok ingʼeyo.’
‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
4 Nimar ma e gima Jehova Nyasaye, Nyasach Israel, wacho kuom ute manie dala maduongʼni kod kuonde dak mar ruodh Juda ma osemuki mondo tigo kaka pidhe kod ligangla
Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
5 kuom kedo gi jo-Babulon: ‘Ginipongʼ-gi gi ringre joma otho mabiro nego gi ich wangʼ mara kod mirimba. Anapand wangʼa ne dala maduongʼni nikech timbegi duto mamono.
a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
6 “‘Kata kamano, anamigi ngima kendo chang; anachang joga kendo anami gibed gi mor kuom kwe mathoth kod rit mogundho.
“‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
7 Anaduog Juda kod Israel koa e twech kendo analosgi gibed kaka ne gin chon.
Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
8 Anapwodhgi kuom richo magisetimona kendo anawenegi richogi duto mag ngʼanyona.
Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
9 Eka dala maduongʼni nomi abed gihuma, ilo, pak kod luor e nyim ogendini duto manie piny mawinjo gik moko duto mabeyo masetimone; kendo ginibed gi luoro mi ginitetni kuom gweth mogundho kod kwe masechiwone.’
Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
10 “Ma e gima Jehova Nyasaye wacho: ‘Uwuoyo kuom dala maduongʼni niya, “Osedongʼ nono chuth, maonge ji kata jamni modakie.” Kata obedo ni mier mag Juda kod yore mag Jerusalem odongʼ nono kamano, maonge ji kata jamni modakie, to ubiro chako winjo,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
11 mor gi ilo kuondego, dwond miaha kod wuon kisera, kod dwond jogo makelo chiwo mar goyo erokamano ne od Jehova Nyasaye. Negiwacho niya, “‘“Goneuru Jehova Nyasaye Maratego erokamano, nimar Jehova Nyasaye ber; herane osiko nyaka chiengʼ.” Nimar anaduog gweth ne piny mane gin-go chon,’ Jehova Nyasaye owacho.
sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
12 “Ma e gima Jehova Nyasaye Maratego wacho: ‘Ka eri, mamono kendo maonge ji kata le, tiende ni e dalane duto nobedi kar kwath ma jokwath kwayoe rombegi.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
13 E dala manie piny gode, mago mantie e tie gode man yo podho chiengʼ kod mago man Negev, mantiere e gwenge mag Benjamin, e mier molworo Jerusalem kod dala mag Juda, rombe nokal kendo e lwet ngʼatno ma kwanogi,’ Jehova Nyasaye owacho.
A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
14 “‘Ndalo biro ma abiro chopo singruokna mar ngʼwono mane aloso gi od Israel kod gi od Juda,’ Jehova Nyasaye ema owacho.
“‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
15 “‘E ndalogo kendo e kindeno anami Bad Yath makare owuog e koth Daudi; enotim gima ratiro kendo nikare e piny.
“‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
16 E ndalogo Juda noresi kendo Jerusalem nodag gi kwe. Ma e nying ma ibiro luongego: Jehova Nyasaye mamiyo wabedo jo-ratiro.’
A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
17 Nimar ma e gima Jehova Nyasaye wacho: ‘Daudi ok nobed maonge gi ngʼato manobedi e kom duongʼ mar od Israel,
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
18 kata jodolo, ma jo-Lawi, bende ok nobed maonge gi ngʼato machungʼ e nyima seche duto mar chiwo misengini miwangʼo pep, ka giwangʼo misengini mag cham kendo chiwo misengini.’”
ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
19 Wach Jehova Nyasaye nobiro ne Jeremia:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
20 “Ma e gima Jehova Nyasaye wacho: ‘Ka inyalo ketho singruokna modiechiengʼ kod singruokna motieno, mondo omi odiechiengʼ kod otieno kik bi e sechegi mowinjore,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
21 bangʼe singruokna gi Daudi jatichna kod singruokna gi jo-Lawi ma gin jodolo ma yalo e nyima inyalo kethi to Daudi ok nobed gi nyakware manobed gi loch e kom duongʼ mare.
to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
22 Anami nyikwa Daudi jatichna kod jo-Lawi ma yalo e nyima bed mangʼeny mokalo akwana ka sulwe manie kor polo kendo ma ok nyal pim ka kwoyo manie dho nam.’”
Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
23 Wach Jehova Nyasaye nobiro ne Jeremia:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
24 “Bende isefwenyo ni jogi wachoni ni, ‘Jehova Nyasaye osekwedo dhoudi ariyo mane oyiero’? Omiyo gijaro joga kendo ok gikawo joga ka oganda achiel.
“Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
25 Ma e gima Jehova Nyasaye wacho: ‘Ka dipo ni pod ok aketo singruokna godiechiengʼ gi otieno kod chike mogurore mar polo kod piny,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
26 eka anakwed nyikwa Jakobo kod Daudi jatichna kendo ok anayier achiel kuom yawuote mondo obed jatelo ewi nyikwa Ibrahim, Isaka kod Jakobo. Nimar anaduognegi mwandugi mi anangʼwon-negi.’”
to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”

< Jeremia 33 >