< Isaya 33 >

1 Unune malit un joma osetieko ji, to pok otieku! Unune malit un joma osendhogo ji, to un pok ondhogu! Ka uweyo tieko ji to notieku; bende ka uweyo ndhogo ji to nondhogu.
Kaitonka, ya kai mai hallakarwa, kai da ba a hallakar da kai ba! Kaitonka, ya maciya amana, kai da ba a ci amanarka ba! Sa’ad da ka daina hallakarwa, za a hallaka ka; sa’ad da ka daina cin amana, za a ci amanarka.
2 Yaye Jehova Nyasaye, yie ikechwa; nimar chunywa dwari. Miwae teko okinyi ka okinyi, kendo bednwa kar resruok, e kinde mag chandruok.
Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.
3 Ka dwondi omor to ji ringo; ka ia malo to ogendini ke.
Da tsawar muryarka, mutane za su gudu; sa’ad da ka tashi, al’ummai za su watse.
4 Yaye un ogendini, mwandu noyaki mana ka kama nyithi bonyo omonjo; kendo ji noyak mwandugi, mana kaka bonyo monjo piny.
Ganimarku, ya al’ummai ƙanana fāri sun girbe; kamar tarin fārin da mutane sun fāɗa wa.
5 Nying Jehova Nyasaye otingʼ malo, nimar odak e polo; obiro pongʼo Sayun gi tim makare kod adiera.
Ubangiji da girma yake, gama yana zaune a bisa; zai cika Sihiyona cikin gaskiya da adalci.
6 Enobed mise mar adier e ndalou, kar mwandu mar resruok gi rieko kod ngʼeyo; luoro Jehova Nyasaye e rayaw mar mwanduni.
Zai zama tabbataccen harsashi na koyaushe, ma’ajin ceto da hikima da sani a yalwace; tsoron Ubangiji shi ne mabuɗin wannan dukiya.
7 To neuru kaka thuondige ywak malit e wangʼ yore; joote ma oseor mondo odwar kwe ywak malit.
Duba, jarumawansu suna kuka da ƙarfi a tituna; jakadun salama suna kuka mai zafi.
8 Yore osedongʼ nono, kendo onge jowuoth e yo. Winjruok osekethi mi joma nobedo joneno ok dew, kendo onge ngʼama omi luor.
An gudu an bar manyan hanyoyi, babu matafiye a kan hanyoyi. Aka keta yarjejjeniya, an rena shaidunsa ba a kuwa ganin girman kowa.
9 Piny ywak kendo dok chien, Lebanon ni e wichkuot kendo okethore, Sharon olokore ongoro ka Araba, kendo Bashan gi Karmel oyaki modongʼ nono.
Ƙasa tana kuka an kuma gudu an bar ta, Lebanon ta sha kunya ta kuma yanƙwane; Sharon ta zama kamar Araba, Bashan da Karmel sun kakkaɓe ganyayensu.
10 Jehova Nyasaye wacho niya, “Koro abiro aa malo, mondo anyisu duongʼna gi tekona.
“Yanzu zan tashi,” in ji Ubangiji. “Yanzu ne za a ɗaukaka ni; yanzu za a ɗaga ni sama.
11 Ubiro mako ich to unywolo yamo; muya muyweyo en mach ma tiekou.
Kun yi cikin yayi, kuka haifi kara; numfashinku wuta ne da zai cinye ku.
12 Ogendini nowangʼ, mi lokre pidhe mag buru, kendo mana kaka kudho mobet e bungu enowangʼ gi mach!”
Za a ƙone mutane kamar da ƙuna farar ƙasa; kamar ƙayayyuwan da aka sare aka kuma sa musu wuta.”
13 Un mudak mabor, winjuru gima asetimo, un mudak machiegni ngʼeuru tekona!
Ku da kuke da nesa, ku ji abin da na yi; ku da kuke kusa, ku san ikona!
14 Joricho man Sayun, kihondko osemako; kibaji ogoyo joma okia nyasaye, mi gisepenjore kendgi niya, “En ngʼa kuomwa manyalo dak kod mach mawengʼo magerni? Koso en ngʼa kuomwa manyalo dak kod mach maliel maonge gikone?”
Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
15 Ngʼatno mawuotho e ratiro kendo wacho gima adiera, ma tamore yudo ohala e yor mecho kendo ok oyie kawo asoya, ngʼatno ma ok chik ite e chenro mar neko, kendo odino wengene e neno timbe mamono,
Shi da yake tafiya cikin adalci yana kuma magana abin da yake daidai, wanda yake ƙin riba daga cuta yana kuma kiyaye hannunsa daga karɓan cin hanci, wanda yake hana kunnuwansa daga ƙulla kisa ya kuma rufe idanunsa a kan tunanin aikata mugunta,
16 ma e ngʼama nodagi kuonde motingʼore gi malo, ma kare mar pondo nobedi got mochiel gohinga motegno. Chiembe ibiro chiw, kendo pi ok nodwon-ne.
shi ne mutumin da zai zauna a bisa, wanda mafakarsa za tă zama kagarar dutse. Za a tanada abincinsa, kuma ruwa ba zai kāsa masa ba.
17 Wengeni biro neno ruoth kober kendo iningʼi piny molandore malach.
Idanunku za su ga sarki a cikin kyansa ku kuma hangi ƙasar da take shimfiɗe can da nisa.
18 E pachi inipar masiche machon: “Ere jatelo maduongʼ cha? Ere ngʼatno mane okawo osuru? Ere jatelo mochungʼne kuonde ngʼicho man malo?”
Cikin tunaninku za ku yi tunani firgitar da ta faru tun dā kuna cewa, “Ina hafsan nan? Ina wannan wanda yake karɓar haraji? Ina hafsan da yake lura da hasumiyoyi?”
19 Ok inichak ine jonjorego kendo, jogo ma wechegi oyombore, kendo mawacho dhok matek winjo.
Ba za ku ƙara ganin waɗannan mutane masu girman kai kuma ba, waɗannan mutane masu magana da harshen da ba ku fahimta ba.
20 Ka irango Sayun, dala maduongʼ mar sewniwa moyier; ibiro neno Jerusalem kama kwe nitie, hema ma ok bi muki; loje mage ok nopudhi, kata tondene ok nochodi.
Ku duba Sihiyona, birnin shagulgulanmu; idanunku za su ga Urushalima, mazauni mai lafiya, tentin da ba za a taɓa gusar ba; wanda ba a taɓa tumɓuke turakunsa ba, ko a tsinke igiyoyinta.
21 Kanyo Jehova Nyasaye biro bedonwa Jal Maratego. Kanyo nochalnwa ka aore kod mago matindo. Yiedhi man-gi tanga ok nokwangʼ kanyo, meli maduongʼ ok nokwangʼ e aore.
A can Ubangiji zai zama Mai Iko Duka namu. Zai zama kamar inda manyan koguna da rafuffuka suke. Matuƙan jirgin ruwa ba za su kai wurinsu ba, manyan jiragen ruwa ba za su yi zirga-zirga a kansu ba.
22 Nimar Jehova Nyasaye e jangʼadnwa bura, Jehova Nyasaye e jaketonwa chik, kendo Jehova Nyasaye e ruodhwa; en ema obiro resowa.
Gama Ubangiji ne alƙalinmu, Ubangiji ne mai ba mu dokoki, Ubangiji ne sarkinmu; shi ne wanda zai cece mu.
23 Tondegi mag meli obwodhore: Tanga ok otwe motegno, ok ginyal kwangʼ maber. Eka gik moyaki ibiro pogi kendo kata mana joma rongʼonde noyud pok.
Maɗaurinku sun kunce ƙarfafan itacen jirgin ba su da kāriya, fikafikan jirgin ba su buɗu ba. Ta haka za a raba yalwar ganima har ma guragu za su kwashe ganimar.
24 Onge ngʼama odak Sayun manowachi niya, “Atuo,” kendo richo mag joma odak kanyo nowenegi.
Ba wani mazauna a Sihiyona da zai ce, “Ina ciwo”; za a kuma gafarta zunuban waɗanda suke zama a can.

< Isaya 33 >