< Hosea 8 >

1 “Ket turumbete e dhogi mondo igo! Ongo ni ewi od Jehova Nyasaye, nikech ji oseketho singruokna kendo gisekwedo chikna.
“Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
2 Jo-Israel noywakna niya, ‘Yaye Nyasachwa, wayangi!’
Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
3 To wasigu biro lawo Israel nikech gisekwedo gima ber.
Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
4 Giketo ruodhi e loch ka ok gipenja; kendo giyiero jotelo ka ok gingʼeyo parona. Giloso nyiseche manono kuom fedha gi dhahabu ma gin-go, to magi kelonegi mana kethruok.
Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
5 Yaye Samaria, wit oko nyasachi mar nyaroya! Mirimba ger kodgi. Nyaka karangʼo ma ok ginyal bedo maler?
Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
6 Gin joma oa Israel! Nyaroyani oselos mana gi lwet dhano omiyo ok en Nyasaye. Nyaroya mar Samaria-no noto matindo tindo.
Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
7 “Gichwoyo yamo to gikayo kalausi. Gin gi cham ma ok ket wiye; kendo ok onyal kelo mogo. To kane onyalo nyago cham, to jopinje mamoko dochame duto.
“Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
8 Israel osetiek duto; kendo sani en e kind ogendini, mana kaka gima nono.
An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
9 Gisedhi nyaka Asuria mana kaka kanyna mar bungu mabayo abaya. Efraim oseusore ne joherane.
Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
10 Kata obedo ni giseusore kendgi e kind ogendini, abiro chokogi kaachiel. Gibiro lal nono kendo enosandgi e bwo loch mar ruoth maratego.
Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
11 “Kata ka obedo ni Efraim nogero kende mangʼeny mag misango mar golo richo, kendegi osebedo mar timo richo.
“Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
12 Ne andiko negi gik mangʼeny mag chikena, to ne gikawogi kaka gigo ma welo kuomgi.
Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
13 Gichiwo misengni mokelna kendo gichamo ring misenginigo, to Jehova Nyasaye ok mor kodgi. Omiyo sani obiro paro anjawo ma gitimo kendo enokumgi kuom richogi. Ginidogi Misri.
Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
14 Jo-Israel wigi osewil gi Jachwechgi, mi gigero ute mag ruodhi; Juda osechielo mier madongo mangʼeny. To anaor mach e miechgi madongogo mitiek kargi mar pondono.”
Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”

< Hosea 8 >