< Hagai 1 >

1 Kane ochopo chiengʼ mokwongo mar dwe mar auchiel, e higa mar ariyo mar loch ruoth Darius, Jehova Nyasaye nowuoyo gi dho janabi Hagai ne Zerubabel wuod Shealtiel, mane jatend piny Juda, gi Joshua wuod Jehozadak, jadolo maduongʼ kowacho niya,
A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
2 Jehova Nyasaye Maratego wacho niya, “Ogendinigi wacho ni, ‘Kinde pok ochopo monego gerne Nyasaye hekalu mare.’”
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
3 Eka wach Jehova Nyasaye nobiro gi dwond janabi Hagai kawacho niya:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
4 “Bende en gima ber adier ka un uwegi udakie uteu mugero mabeyo, to hekalu marani to omukore machal kama?”
“Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
5 Ma emomiyo Jehova Nyasaye Maratego wacho niya, “Nonuru timbeu.
To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
6 Usechwoyo mangʼeny, to ukayo mana matin; uchiemo, to gima uchamo ok nyal yiengʼou, umetho, to ok romu; urwakoru gi lewni, to onge kata ngʼato achiel kuomu mayudo liet; to nyaka un joma nwangʼo chudo, bangʼ ka unwangʼo chudo to uketo mana ei ofuku motuch.”
Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
7 Jehova Nyasaye Maratego wacho niya, “Nonuru timbeu.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
8 Idh-uru udhi e gode mondo ukel yien ugernago ot manyalo morgo, kama duongʼna maler nyalo nenoree,” Jehova Nyasaye owacho.
Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
9 “Usegombo yudo mangʼeny, to osetamore ma uyudo mana matin; to kata mana mano mago ma usechoko mukeloe dala, abiro kudho oko. Mani notimore nikech angʼo?” Jehova Nyasaye Maratego penjo. “Nikech hekaluna ma uweyo odongʼ gunda, ka un uwegi to uringo kudhi e uteu molos mabeyo.
“Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
10 Mano emomiyo koro Polo malo ok nyal miyou koth kata matin, kendo piny osiko mana kotwo ma ok nyal nyago gimoro.
Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
11 Mano emomiyo osehononu oro mondo otwo piny kaachiel gi gode, mi cham gi mzabibu kod mo zeituni, gi gik moko duto ma piny nyago ner, mondo kech omak dhano gi jamni, kendo oketh tije duto ma dhano oloso.”
Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
12 Eka Zerubabel ma wuod Shealtiel kod Joshua wuod Jehozadak, ma jadolo maduongʼ, kaachiel gi ji mamoko mane oa e twech, kane giwinjo weche Nyasaye gi weche mag janabi Hagai, kaka Jehova Nyasaye ne oore, luoro maduongʼ nomakogi e nyim Ruoth.
Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
13 Eka Hagai jaote mar Jehova Nyasaye, nowuoyo kod ji konyisogi weche mane Jehova Nyasaye omiye, kowacho niya, “An kodu,” Jehova Nyasaye owacho.
Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
14 Eka Jehova Nyasaye nojiwo chuny Zerubabel wuod Shealtiel mane jatend piny Juda, chuny Joshua, kod chuny joma moko mane oa e twech. Negibiro kendo gichako tich e od Jehova Nyasaye Maratego ma Nyasachgi,
Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
15 tarik piero ariyo gangʼwen e dwe mar auchiel e higa mar ariyo mar loch Ruoth Darius.
a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,

< Hagai 1 >