< Chakruok 46 >

1 Kuom mano Israel nowuok kod gige duto, kendo kane ochopo Bersheba, notimo misango ne Nyasach Isaka wuon-gi.
Saboda haka Isra’ila ya kama hanya da dukan abin da yake nasa, sa’ad da ya kai Beyersheba, sai ya miƙa hadayu ga Allah na Ishaku, mahaifinsa.
2 Kendo Nyasaye nowuoyogi Israel e fweny gotieno kendo owachone niya, “Jakobo! Jakobo!” Nodwoke niya, “Antie.”
Allah kuwa ya yi magana ga Isra’ila a wahayi da dare ya ce, “Yaƙub! Yaƙub!” Yaƙub kuwa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
3 Nyasaye nowachone niya, “An Nyasaye ma Nyasach wuonu. Kik iluor dhi Misri, nikech anami ibedi oganda maduongʼ kuno.
Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah, Allah na mahaifinka. Kada ka ji tsoron zuwa Masar, gama zan mai da kai al’umma mai girma a can.
4 Abiro dhi kodi Misri kendo nachak aduogi ka adier kendo Josef ema noyuo wangʼi sa thoni.”
Zan gangara zuwa Masar tare da kai, tabbatacce zan sāke dawo da kai. Kuma hannun Yusuf zai rufe idanunka.”
5 Eka Jakobo nowuok Bersheba, kendo yawuot Israel noketo wuon-gi kod nyithindgi, kod mondgi e geche mane Farao oseorone.
Sa’an nan Yaƙub ya bar Beyersheba,’ya’yan Isra’ila maza, suka ɗauki mahaifinsu Yaƙub da’ya’yansu da matansu a cikin wagonun da Fir’auna ya aika don a kawo shi.
6 Negikawo jambgi kod mwandugi mane giseyudo e piny Kanaan, kendo Jakobo kod nyikwaye duto nodhi Misri.
Suka kuma ɗauki dabbobinsu da mallakarsu, da suka samu a Kan’ana, Yaƙub kuwa da dukan zuriyarsa suka tafi Masar.
7 Nodhi Misri gi yawuote gi nyige kod nyikwaye ma yawuowi kod ma nyiri.
Ya ɗauki’ya’yansa maza da jikokinsa da’ya’yansa mata da jikokinsa mata, dukan zuriyarsa zuwa Masar.
8 Magi e nying yawuot Israel (ma tiende ni Jakobo kod nyikwaye) mane odhi Misri. Reuben ema ne wuod Jakobo makayo.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza (Yaƙub da zuriyarsa) waɗanda suka tafi Masar, Ruben ɗan farin Yaƙub.
9 Yawuot Reuben ne gin: Hanok, Palu, Hezron kod Karmi.
’Ya’yan Ruben maza su ne, Hanok, Fallu, Hezron da Karmi.
10 Yawuot Simeon ne gin: Jemuel, Jamin, Ohad, Jakin, Zohar kod Shaul mane wuod nyar Kanaan.
’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana.
11 Yawuot Lawi ne gin: Gershon, Kohath kod Merari.
’Ya’yan Lawi maza su ne, Gershon, Kohat da Merari.
12 Yawuot Juda ne gin: Er, Onan, Shela, Perez kod Zera (to Er kod Onan ne otho e piny Kanaan). Yawuot Perez ne gin: Hezron kod Hamul.
’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan, Shela, Ferez da Zera (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan’ana).’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul.
13 Yawuot Isakar ne gin: Tola, Pua, Jashub kod Shimron.
’Ya’yan Issakar maza su ne, Tola, Fuwa, Yoshub da Shimron.
14 Yawuot Zebulun ne gin: Sered, Elon kod Jalel.
’Ya’yan Zebulun maza su ne, Sered, Elon da Yaleyel.
15 Magi e yawuowi mane Lea onywolo ne Jakobo e piny mar Padan Aram, ka ok okwan Dina nyare. Yawuote kod nyige duto ne piero adek gadek.
Waɗannan su ne’ya’yan Liyatu maza da ta haifa wa Yaƙub a Faddan Aram, ban da’yarsa Dina.’Ya’yansa maza da mata duka, mutum talatin da uku ne.
16 Yawuot Gad ne gin: Zefon, Hagi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi kod Areli.
’Ya’yan Gad maza su ne, Zafon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi da Areli.
17 Yawuot Asher ne gin: Imna, Ishva, Ishvi kod Beria. Nyamin-gi ne en Sera. Yawuot Beria ne gin: Heber kod Malkiel.
’Ya’yan Asher maza su ne, Imna, Ishba, Ishbi da Beriya.’Yar’uwarsu ita ce Sera.’Ya’yan Beriya maza su ne, Heber da Malkiyel.
18 Magi e nyithindo mane Zilpa, jatich mane Laban omiyo nyare Lea onywolo ne Jakobo. Giduto ne gin nyithindo apar gauchiel.
Waɗannan su ne’ya’yan da Zilfa ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Liyatu.’Ya’yan duka, su sha shida ne.
19 Yawuot Rael chi Jakobo ne gin: Josef kod Benjamin.
’Ya’yan Yaƙub maza waɗanda Rahila ta haifa su ne, Yusuf da Benyamin.
20 Asenath nyar Potifera, jadolo mar On nonywolone Josef Manase kod Efraim e piny Misri.
A Masar, Asenat’yar Fotifera, firist na On ta haifi Manasse da Efraim wa Yusuf.
21 Yawuot Benjamin ne gin: Bela, Beker, Ashbel, Gera, Naaman, Ehi, Rosh, Mupim, Hupim kod Ard.
’Ya’yan Benyamin maza su ne, Bela, Beker, Ashbel, Gera, Na’aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim da Ard.
22 Magi e yawuowi mane Rael onywolone Jakobo. Giduto ne gin ji apar gangʼwen.
Waɗannan su ne’ya’yan Rahila maza waɗanda ta haifa wa Yaƙub, dukansu mutum goma sha huɗu ne.
23 Wuod Dan ne en Hushim.
Yaron Dan shi ne, Hushim.
24 Yawuot Naftali ne gin: Jaziel, Guni, Jezer kod Shilem.
’Ya’yan Naftali maza su ne, Yazeyel, Guni, Yezer da Shillem.
25 Magi e yawuowi mane Bilha, jatich mane Laban omiyo Rael nyare onywolone Jakobo. Giduto ne gin ji abiriyo.
Waɗannan su ne’ya’ya mazan da Bilha ta haifa wa Yaƙub, ita ce Laban ya ba wa’yarsa Rahila.’Ya’yan suka su bakwai ne.
26 Ji duto mane odhi gi Jakobo Misri, tiende ni nyithinde hie ka ok okwan mond yawuote ji piero auchiel gi auchiel.
Dukan waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub, waɗanda suke zuriyarsa kai tsaye ban da matan’ya’yansa maza, su mutum sittin da shida ne.
27 Joka Jakobo duto mane odhi Misri ne gin ji piero abiriyo koriwore gi yawuowi ariyo mane Josef onywolo Misri.
In aka haɗa da’ya’yan nan maza guda biyu waɗanda aka haifa wa Yusuf a Masar, membobin iyalin Yaƙub, waɗanda suka tafi Masar, duka su saba’in ne.
28 Omiyo Jakobo nooro Juda mondo odhi ir Josef mondo obi oromnegi ka gidhi Goshen. Kane gichopo e gwengʼ mar Goshen,
To, Yaƙub ya aiki Yahuda yă yi gaba yă sadu da Yusuf, don yă nuna musu hanyar da za su bi zuwa yankin Goshen. Da suka isa yankin Goshen,
29 Josef noiko gache kendo oikore mar dhi Goshen mondo odhi oromne wuon-gi Israel. Kane Josef ochopo ire, nokwako wuon-gi kendo oywak kuom kinde malach.
sai Yusuf ya kintsa keken yaƙinsa ya haura zuwa Goshen don yă taryi mahaifinsa, Isra’ila. Nan da nan da isowar Yusuf a wurin mahaifinsa, sai ya rungumi mahaifinsa, ya yi kuka na dogon lokaci.
30 Israel nowacho ne Josef niya, “Koro kata ka atho, to onge wach, nikech aseneno an awuon ni kara pod ingima.”
Isra’ila ya ce wa Yusuf, “Yanzu ina a shirye in mutu, da yake na gani da kaina cewa har yanzu kana da rai.”
31 Eka Josef nowacho ne owetene kod jood wuon mare duto niya, “Abiro dhi mondo awuo gi Farao kendo abiro wachone ni, ‘Owetena kod jood wuora duto mane odak e piny Kanaan osebiro ira.
Sa’an nan Yusuf ya ce wa’yan’uwansa da gidan mahaifinsa, “Zan haura in yi magana da Fir’auna, zan kuwa ce masa, ‘’Yan’uwana da gidan mahaifina, waɗanda suke zaune a ƙasar Kan’ana, sun zo wurina.
32 Jogi gin jokwath; gikwayo jamni, kendo gisebiro kod kwethgi kod dhogi kod gigegi duto.’
Mutanen fa, makiyaya ne; suna kiwon dabbobi, sun kuma zo tare da garkunansu da shanunsa da kuma kome da suka mallaka.’
33 Ka Farao oluongou kendo openjou ni, ‘Utiyo angʼo?’
Sa’ad da Fir’auna ya kira ku ciki, ya yi tambaya, ‘Mece ce sana’arku?’
34 to nyaka uwachne ni, ‘Jotichgi osebedo jokwath chakre tindowa, mana kaka kwerewa notimo.’ Eka ibiro yienu mondo udag e gwengʼ Goshen, nikech jo-Misri ok ohero jokwath.”
Ku amsa, ‘Bayinka suna kiwon dabbobi ne, tun muna samari har zuwa yanzu, kamar yadda kakanninmu suka yi.’ Ta haka za a bar ku ku zauna a yankin Goshen, gama Masarawa suna ƙyamar makiyaya.”

< Chakruok 46 >