< Chakruok 35 >
1 Eka Nyasaye nowacho ne Jakobo niya, “Aa malo idhi Bethel kendo idag kuno mi iger kendo mar misango ne Nyasaye, mane ofwenyoreni kane iringo ia kuom Esau owadu.”
Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
2 Kuom mano Jakobo nowacho ne joode duto kod ji mane ni kode niya, “Wituru nyiseche mag pinje mamoko ma un-go kendo upwodhru mi urwak lewni maler.
Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
3 Eka ubi mondo wadhiuru Bethel, kuma abiro dhi geroe kendo mar misango ne Nyasaye, mane odwoka e kinde mane an e chandruok malich kendo ma osebedo koda kamoro amora ma asedhiyoe.”
Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
4 Kuom mano negimiyo Jakobo nyiseche mag pinje mamoko mane gin-go kod stadi mane ni e itgi kendo Jakobo noyikogi e tiend yiend ober man Shekem.
Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
5 Eka negichako wuoth kendo luoro mar Jehova Nyasaye nomako mier duto mane okiewo kodgi maonge ngʼama nolawo bangʼ-gi.
Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
6 Jakobo kod ji duto mane ni kode nochopo Luz (ma tiende ni Bethel) e piny Kanaan.
Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
7 Kanyo Jakobo nogero kendo mar misango kendo noluongo kanyo ni El Bethel, nikech kanyo ema ne Nyasaye ofwenyorene kane oringo owadgi.
A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
8 Debora, ma japit Rebeka notho kendo noyike e tiend yiend ober machiegni gi Bethel. Kuom mano nochak kanyo ni Allon Bakuth.
To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
9 Bangʼ ka Jakobo nosea Padan Aram, Nyasaye nochako ofwenyorene kendo nogwedhe.
Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
10 Nyasaye nowachone niya, “Kata obedo ni nyingi en Jakobo to ok nochak oluongi kamano to koro ibiro luongi ni Israel.” Omiyo nochake ni Israel.
Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
11 Kendo Nyasaye nowachone niya, “An Nyasaye Maratego, nywolri kendo imedri. Ogendini kod dhout ogendini noa kuomi kendo ruodhi nowuog kuomi.
Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
12 Piny mane amiyo Ibrahim kod Isaka bende abiro miyi kaachiel gi nyikwayi.”
Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
13 Eka Nyasaye nodhi e polo moweye kama ne giwuoyoe kodeno.
Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
14 Jakobo nochungo siro mar kidi kanyono mane Nyasaye owuoyoe kode, kendo noolo ewi sirono misango miolo piny bende noolo misango mar mo ewi siro.
Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
15 Jakobo nochako kanyo mane Nyasaye owuoyoe kodeno ni Bethel.
Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
16 Eka negiwuok gia Bethel. Kane gisedhi mochwalore gi Efrath, muoch nochako kayo Rael kendo nochandore ahinya.
Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
17 E kinde mane muoch kayeno, jacholo nowachone niya, “Kik iluor nikech inywolo wuowi machielo.”
Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
18 Kane chunye chiegni chot nochako wuodeno ni Ben-Oni. To wuon mare to nochake ni Benjamin.
Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
19 Kuom mano Rael notho kendo nokunye e yo madhi Efrath (ma tiende ni Bethlehem).
Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
20 Jakobo noketo siro ewi liend Rael kendo nyaka chil kawuono sirono obet kar liend Rael.
Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
21 Israel nochako odhi nyime giwuoth kendo noguro hembe tok oinga mar Migdal Eder.
Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
22 Kane oyudo Israel dak kuno, Reuben nodhi moterore gi Bilha jatich ma nyako mar wuon-gi mi Israel nowinjo wachno. Jakobo ne nigi yawuowi apar gariyo:
Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
23 Yawuot Lea ne gin: Reuben wuod Jakobo makayo, Simeon, Lawi, Juda, Isakar kod Zebulun.
’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
24 Yawuot Rael ne gin: Josef kod Benjamin.
’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
25 Yawuot Bilha, jatich Rael madhako ne gin: Dan kod Naftali.
’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
26 Yawuot Zilpa jatich Lea madhako ne gin: Gad kod Asher. Magi ema ne yawuot Jakobo mane onywolone Padan Aram.
’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
27 Jakobo noduogo dala ir wuon-gi Isaka Mamre machiegni gi Kiriath Arba (ma tiende ni Hebron), kumane Ibrahim kod Isaka odakie.
Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
28 Isaka nodak higni mia achiel gi piero aboro.
Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
29 Eka Isaka notho kendo noluwo kwerene ka oti kendo hike ngʼeny. Kendo yawuot Esau kod Jakobo noyike.
sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.