< Wuok 19 >

1 E dwe mar adek bangʼ ka jo-Israel nosewuok Misri, negichopo e thim Sinai e odiechiengʼno.
A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
2 Bangʼ kane gisewuok Refidim, negidonjo thim Sinai, kendo Israel nojot e nyim got e thimno.
Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
3 Eka Musa noidho got mondo odhi owuo gi Nyasaye kendo Jehova Nyasaye noluonge gi ewi got mowachone kama: “Ma e gima iwachne od Jakobo to gi jo-Israel.
Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
4 ‘Un uwegi useneno gima ne atimone piny Misri kendo kaka ne atingʼou mana kaka ongo tingʼo nyithinde mi akelou ira awuon.
‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
5 Koro, ka uwinja chuth mi urito singruokna, to kuom ogendini duto ubiro bedo mwanduna awuon. Kata obedo ni piny duto en mara,
Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
6 un to ubiro bedona oganda mar jodolo kendo oganda maler.’ Magi e weche manyaka iwachne jo-Israel.”
za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
7 Kuom mano Musa nodok moluongo jodongo duto mag oganda mi oketo e nyimgi weche duto mane Jehova Nyasaye ochike mondo owachi.
Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
8 Oganda duto nodwoko kanyakla kawacho niya, “Wabiro timo gik moko duto ma Jehova Nyasaye ochiko.” Kuom mano Musa nodwoko wachgi ne Jehova Nyasaye.
Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
9 Jehova Nyasaye nowacho ne Musa niya, “Abiro biro iru e boche polo mondo omi oganda owinj kaka awuoyo kodi kendo mano biro miyo giket genogi kuomi ndalo duto.” Eka Musa nonyiso Jehova Nyasaye gima oganda nowacho.
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
10 Kendo Jehova Nyasaye nowacho ne Musa niya, “Dhi ir oganda mondo ipwodhgi kawuono gi kiny. Ketgi giluok lepgi
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
11 mondo gibed moikore e odiechiengʼ mar adek, nimar chiengʼno Jehova Nyasaye biro lor ewi Got Sinai ka ji duto nene.
Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
12 Ket tongʼ ne oganda molworo got kendo nyisgi ni, ‘Beduru motangʼ mondo kik ngʼato idh got kata mulo tie got, nimar ngʼato angʼata mochopo e tiend godni to nyaka negi.
Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
13 Ngʼatno nyaka chiel gi kite, kata chwowe gi asere; to kik ngʼato angʼata ket lwete kuome. Bed ni en dhano kata le, ok noweye mondo obed mangima.’ To ji nyalo idho godno mana ka tungʼ oywak kuom thuolo malach.”
Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
14 Bangʼ ka Musa noselor e got modhi ir oganda, nopwodhogi mine gilwoko lepgi.
Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
15 Eka nowacho ne oganda niya, “Ikreuru ne odiechiengʼ mar adek kendo kik ngʼato riwre gi chiege.”
Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
16 Chiengʼ mar adek gokinyi, polo nomil kamor, ka boche polo okwako wi got kendo turumbete noywag matek, ma ji duto mane ni e kambi notetni.
A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
17 Eka Musa notelo ne oganda kawuok e kambi mondo orom gi Nyasaye, kendo negichungʼ e tiend got.
Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
18 Iro noimo Got Sinai nikech Jehova Nyasaye nolor kanyo ei mach. Iro ne dhwolore kawuok ewi godno mana ka iro mawuok e kendo, mi got duto noyiengni,
Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
19 kendo turumbete nomedo ywak matek. Eka Musa nowuoyo kendo Nyasaye nodwoke.
sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
20 Jehova Nyasaye nolor ewi Got Sinai mi oluongo Musa nyaka ewi godno. Omiyo Musa noidho e got
Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
21 mi Jehova Nyasaye nowachone niya, “Dhiyo kendo isiem ji mondo kik girire ni gidwaro neno Jehova Nyasaye nimar thothgi nyalo tho.
sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
22 Kata mana jodolo ma osudo ir Jehova Nyasaye nyaka pwodhre ka ok kamano to Jehova Nyasaye nomwomre kuomgi.”
Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
23 Musa nowacho ne Jehova Nyasaye niya, “Ji ok nyal biro ewi Got Sinai nimar in iwuon ema ne isiemowa ni mondo waket kiewo molworo got mondo owale obed maler.”
Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
24 Jehova Nyasaye nodwoke niya, “Lor piny iom Harun ibigo ira. To jodolo gi ji kik rire mondo one Jehova Nyasaye, nono to abiro mwomora kuomgi.”
Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
25 Kuom mano Musa nolor piny ir ji monyisogi gik mane Jehova Nyasaye owachone.
Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.

< Wuok 19 >