< 1 Samuel 9 >

1 Ne nitie ja-Benjamin moro mongʼere ma nyinge Kish wuod Abiel, ma wuod Zeror, ma wuod Bekorath, ma wuod Afia ma ja-Benjamin.
An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
2 Ne en gi wuowi miluongo ni Saulo, ne en rawera ma jaber e kind jo-Israel bende ne en rabora ma ji moko ne rem mana e goke.
Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
3 Chiengʼ moro punde mag Kish wuon Saulo nolal kendo Kish nowachone wuode ma Saulo niya, “Kaw achiel kuom jotich mondo udhigo udwar punde.”
To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
4 Omiyo nokadho e piny got mar Efraim kod alwora mar Shalisha, to ok ne giyudogi. Negidhiyo ma gichopo e gwenge mag Shaalim, to punde ne onge kuondego. Eka nokadho e piny Benjamin, to ne ok giyudogi.
Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
5 Kane gichopo e gwenge mag Zuf, Saulo nowachone jatich mane ni kode niya, “Bi wadogi, dipo ka wuora oweyo paro punde kendo mochako mana parowa.”
Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
6 To jatich nodwoke kawachone niya, “Iwinjo, e dalano nitiere ngʼat Nyasaye moro marahuma kendo gik mowacho duto timore mana kaka owacho. Bi wadhi ire koro nikech onyalo nyisowa yo monego waluw.”
Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
7 Saulo nowachone jatich niya, “To ka wadhi, en angʼo ma wabiro miyo ngʼatni? Chiemo mane ni e mifukewa oserumo. Waonge kod mich ma wanyalo tero ne ngʼat Nyasaye. En angʼo ma wan-go?”
Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
8 Jatich nowachone kendo niya, “An-gi pesa moko manok. Abiro miye ngʼat Nyasaye mondo onyiswa yo monego waluw.”
Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
9 Chon e piny Israel kane ngʼato dhi penjo Nyasaye wach ne owacho niya, “Bi wadhi ka Janen,” nikech ngʼat miluongo ni janabi ndaloni ne iluongo ni janen.
(A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
10 Saulo nowachone jatich niya, “Mano ber, bi wadhi.” Omiyo negiwuok ma gidhi e dala kama ngʼat Nyasaye nodakie.
Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
11 Kane giidho got matin-no ka gichomo dalano negiromo gi nyiri moko kadhi umbo pi kendo ne gipenjogi niya, “Bende ngʼat makoro nika?”
Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
12 To negidwoko niya, “Ee entie, ero odhi nyimu kanyo, returu. Koro eka odonjo e dalawa kawuono nimar jowa timo misango e kama owal.”
’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
13 E sa ma usedonjo e dala to ubiro yudo kapok oidho odhi malo kama owal mondo ochiem. Ji ok bi chako chiemo nyaka ochopi, nikech nyaka ogwedh gir timo misango eka bangʼe jomo oluongi nyalo chiemo. Returu mapiyo sani ema unyalo yude.
Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
14 Ne giwuotho mi gidhi nyaka dala, to kane gidonjo kanyo to negineno Samuel, kabiro gwenyore kodgi kochiko kama owal.
Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
15 To chiengʼ motelone biro mar Saulo, noyudo ka Jehova Nyasaye osefwenyo ma ne Samuel.
Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
16 “Kiny kar sa ma kama abiro oro ngʼato moa e piny Benjamin. Wire mondo otel ne joga ma jo-Israel, enores joga e lwet jo-Filistia. Asekecho joga nimar ywakgi osechopona.”
“Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
17 Kane Samuel ogoyo wangʼe kuom Saulo, Jehova Nyasaye ne owachone niya, “Ma e ngʼat mane awuoyoni kuome nibiro rito ogandana.”
Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
18 Saulo nodhi ir Samuel e dhorangach mopenje niya, “Kiyie to nyisa od janen?”
Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
19 Samuel nodwoke niya, “An e janen. Tel nyima idhi kama owal maler nimar kawuono ibiro chiemo koda kendo kiny gokinyi abiro weyi idhi kendo ananyisi mago duto man e chunyi.
Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
20 Kor ka wach punde mane olal ndalo adek mokadho to owe chandi nimar oseyudgi. Koso en ngʼa ma chuny jo-Israel duto dwaro ka ok en in gi od wuonu?”
Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
21 Saulo nodwoko niya, “Donge an ja-Benjamin, oganda matin ahinya ei Israel, to donge dhoodwa bende e dhoot matin, moloyo ei oganda mar Benjamin? Angʼo momiyo iwacho wechegi kuoma?”
Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
22 Eka Samuel nokelo Saulo gi jatije kar budho moketogi gibet e kom manyime kuom ji duto mane oluongo mane nyalo romo ji piero adek.
Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
23 Samuel ne onyiso jatedo niya, “Kel lemo mar ringʼo mane amiyi, mane anyisi ni iket tenge.”
Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
24 Eka jatedo nokawo em gi sembe moketo e nyim Saulo. Samuel nowacho niya, “Ma e gima nokan-ni, cham, nikech nokan-nigo ne nyasini, chakre e kinde mane aluongoe welo.” Eka Saulo nochiemo gi Samuel chiengʼno.
Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
25 Kane gisea e kama owal mi gidwogo e dala, Samuel nowuoyo gi Saulo ka gin kode ewi ode malo.
Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
26 Ne gichiewo ka piny yawore, eka Samuel noluongo Saulo ewi ot, kowachone niya, “Ikri abiro gonyi mondo ichak wuodhi.” Kane Saulo oseikore, en kod Samuel ne giwuok oko.
Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
27 Kane oyudo gin e bath dala, Samuel nowachone Saulo niya, “Nyis jatichni mondo otel, in to dongʼ chien mondo amiyi wach moa kuom Nyasaye.” Omiyo jatijno notimo kamano.
Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”

< 1 Samuel 9 >