< 1 Samuel 4 >

1 Kendo wach Samuel nochopo ne jo-Israel duto. Noyudo jo-Israel odhi kedo gi jo-Filistia. Jo-Israel ne ogo kambi Ebeneza to jo-Filistia to nogo kambi Afek.
Duk sa’ad da Sama’ila ya yi magana dukan Isra’ila sukan saurare shi. Isra’ilawa suka fita yaƙi da Filistiyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani a Ebenezer, Filistiyawa kuma a Afek.
2 Jo-Filistia noyaro ne lweny mondo orom gi jo-Israel, kendo lweny nolandore. Jo-Israel ne olo gi jo-Filistia mine ginego ji madirom alufu angʼwen e paw lweny.
Filistiyawa suka tunƙuro mayaƙansu domin su sadu da Isra’ilawa, yaƙi kuwa ya yi tsanani har Isra’ilawa suka sha kashi a hannun Filistiyawa. Filistiyawa suka kashe Isra’ilawa kusan mutum dubu huɗu a bakin dāgā.
3 Kane jolweny odwogo e kambi, jodong Israel nopenjogi niya, “Angʼo momiyo Jehova Nyasaye oseweyo jo-Filistia oloyowa kawuononi? Waomuru Sandug Muma mar Singruok mar Jehova Nyasaye man Shilo, mondo odhi kodwa kendo oreswa e lwet wasikwa.”
Lokacin da mayaƙan suka komo sansani, dattawan Isra’ilawa suka yi tambaya suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa muka sha ɗibga a hannun Filistiyawa? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo. Domin yă tafi tare da mu yă ba mu nasara kan abokan gābanmu.”
4 Eka oganda nooro jomoko mondo odhi Shilo kendo negidwogo gi Sandug Muma mar Singruok mar Jehova Nyasaye Maratego, mobedo e kind kerubi. Kendo yawuot Eli ariyo ma gin Hofni gi Finehas nobiro gi Sandug Muma mar Singruok mar Nyasaye.
Saboda haka mutanen suka aika waɗansu maza zuwa Shilo, suka kuwa tafi suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji Maɗaukaki wanda yake zaune tsakanin Kerubobi.’Ya’yan Eli biyun nan Hofni da Finehas suna wurin tare da akwatin alkawarin Ubangiji.
5 Kane Sandug Muma mar Singruok mar Jehova Nyasaye ochopo e kambi, jo-Israel duto nokok matek ma piny noyiengni.
Da aka shigo da akwatin alkawarin Ubangiji a cikin sansani, sai Isra’ilawa suka tā da babbar murya har ƙasa ta jijjiga.
6 Jo-Filistia kane owinjo koko negipenjo niya, “Mano to koko manade magore e kambi mar jo-Hibrania?” Kane gifwenyo ni Sandug Muma mar Singruok mar Jehova Nyasaye osekel e kambi,
Da jin wannan, Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Me ke kawo wannan ihu mai ƙarfi haka a sansanin Isra’ilawa?” Da suka gane cewa akwatin alkawarin Ubangiji ne ya shiga sansanin,
7 jo-Filistia nobedo maluor kagiwacho niya, “Nyasaye osebiro e kambi. Wan gi chandruok! Gima kama pok otimore nyaka nene.
sai Filistiyawa suka ji tsoro, suka ce, “Wani allah ya shiga cikin sansanin. Mun shiga uku! Ba a taɓa yin wani abu haka ba.
8 To mano kaka wan gi masira! En ngʼa mabiro resowa e lwet nyiseche maratekegi? Gin nyiseche mane ogoyo jo-Misri gi masiche mayoreyore e thim.
Kaiton mu! Wa zai kuɓutar da mu daga hannun waɗannan manyan alloli? Su ne allolin da suka buga Masarawa da irin annoba masu yawa a jeji.
9 Beduru motegno un jo-Filistia! Beduru gi chir kaka chwo ka ok kamano to udhi bedo wasumb jo-Hibrania mana kaka gisebedonu. Omiyo beduru jochir kendo ukedi!”
Ku yi ƙarfin hali, ku yi mazantaka, ku Filistiyawa, domin kada ku zama bayin Ibraniyawa kamar yadda suke a gare ku. Ku yi mazantaka, ku yi yaƙi.”
10 Omiyo jo-Filistia nokedo kendo, jo-Israel nolo mi ngʼato ka ngʼato noringo kadhi e hembe. Noneg ji mathoth ahinya! Noneg jolweny mag jo-Israel alufu piero adek.
Saboda haka Filistiyawa suka yi yaƙi, Isra’ilawa kuwa suka sha ɗibga, kowane mutum kuwa ya gudu zuwa tentinsa. Kisan kuwa ya yi muni ƙwarai. Isra’ilawa sun rasa mayaƙa dubu talatin.
11 Sandug Muma mar Nyasaye ne okaw, yawuot Eli ariyo Hofni gi Finehas ne onegi.
Aka ƙwace akwatin alkawarin Ubangiji. Aka kuma kashe’ya’yan Eli biyu, Hofni da Finehas.
12 Chiengʼ onogo ja-Benjamin moro noringo koa e lweny modhi Shilo, lepe ne oyiech kendo wiye notimo buru.
A wannan rana wani mutumin Benyamin ya ruga da bakin dāgā ya shigo Shilo, taguwarsa a yage, kansa kuma a rufe da ƙasa.
13 Kane ochopo, nonwangʼo Eli kobet e kome e dir yo, ka orito nimar luoro nomake nikech Sandug Muma mar Nyasaye. Kane ngʼatno odonjo e dala mowacho gima ne osetimore, ji duto mane ni ei dala nomuoch gi nduru.
Da ya iso sai ga Eli zaune a kujera kusa da hanya yana kallo, domin tsoron da yake da shi saboda akwatin alkawarin Allah. Da mutumin ya shigo a garin ya ba da labarin abin da ya faru sai dukan gari ya ruɗe da ihu.
14 Eli nowinjo nduru mopenjo niya, “Nduru magoreni nyiso angʼo?” Ngʼatno noreto piyo kodhi ir Eli ma hike
Eli ya ji ihun ya yi tambaya ya ce, mene ne dalilin wannan ihu? Mutumin ya rugo wurin Eli,
15 ne oseromo higni piero ochiko gaboro kendo wengene nosedinore makoro ok onen.
wanda yake da shekaru tasa’in da takwas da haihuwa, idanunsa kuma ƙarfi ya ƙare, baya iya gani.
16 Nowachone Eli niya, “Aringo ka awuok kar lweny mana kawuononi.” Eli nopenjo niya, “Angʼo motimore wuoda?”
Mutumin ya gaya wa Eli cewa, “Shigowata ke nan daga bakin dāgā. Na kuɓuce daga can yau ɗin nan.” Eli ya ce, “Me ya faru da’ya’yana?”
17 Ngʼat mane okelo wach nodwoko niya, “Israel nolo gi jo-Filistia, kendo jolweny otho mangʼeny. Koda ka yawuoti ariyo, Hofni gi Finehas osetho, to Sandug Muma mar Nyasaye okaw modhi.”
Mutumin da ya kawo labarin ya ce, “Isra’ilawa sun gudu a gaban Filistiyawa, mayaƙan kuma sun sha mummunar ɗibga.’Ya’yanka Hofni da Finehas su ma sun mutu. Aka kuma ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
18 Kane ohulo wach mar Sandug Muma mar Nyasaye, Eli nogore piny ataro koa e kom manobetie e bath rangach. Ngʼute ne otur mi notho, nikech ne oti kendo ne ochwe. Ne osetelo ne Israel kuom higni piero angʼwen.
Da ya ambaci akwatin alkawarin Allah, sai Eli ya fāɗi da baya daga kujeransa kusa da ƙofa, wuyarsa ta karye, ya kuma mutu domin ya tsufa ƙwarai. Ya yi shugabancin Isra’ila shekaru arba’in.
19 Chi wuode, ma jaod Finehas, ne nigi ich mochiegni nywol. To kane owinjo wach ni Sandug Muma mar Nyasaye osekaw kendo ni kwar mare gi chwore osetho, muoch nochako kaye mi nonywol, kata kamano nywolne nobiro marach.
Matar Finehas, ɗansa tana da ciki a lokacin ta kuma kusa haihuwa. Sa’ad da ta ji labari cewa an ƙwace akwatin alkawarin Allah, ta kuma labarin surukinta da mijinta sun mutu, sai ta shiga naƙuda, ta kuma haihu. Amma naƙuda ta sha ƙarfinta.
20 Kane odwa tho, mon mane chole nowachone niya, “Kik iluor nikech isenywolo wuowi.” To ne ok odwokogi kata dewogi.
Da tana mutuwa, matan da suke lura da ita suka ce, “Kada ki karaya kin haifi ɗa namiji.” Amma ba tă ba da amsa ko tă kula ba.
21 Nochako nyathi ma wuowino ni Ikabod kowacho niya, “Duongʼ oseweyo Israel, nikech negikawo Sandug Muma mar Nyasaye kod tho mar kwar mare gi mar chwore.”
Ta ba wa yaron suna Ikabod, ma’ana “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila”, domin an ƙwace akwatin alkawarin Allah, domin kuma mutuwar surukinta da na mijinta.
22 Nowacho niya, “Duongʼ oseweyo Israel, nimar Sandug Muma mar Nyasaye osekaw.”
Ta ce, “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila, gama an ƙwace akwatin alkawarin Allah.”

< 1 Samuel 4 >