< Zakarias 1 >
1 I den ottende Måned i Darius's andet Regeringsår kom HERRENs Ord til Profeten Zakarias, en Søn af Berekja, en Søn af Iddo, således:
A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
2 HERREN var fuld af Harme imod eders Fædre.
“Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
3 Men sig til dem: Så siger Hærskarers HERRE: Vend om til mig, lyder det fra Hærskarers HERRE, så vil jeg vende om til eder, siger Hærskarers HERRE.
Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Vær ikke som eders Fædre, til hvem de tidligere Profeter talte således: Så siger Hærskarers HERRE: Vend om fra eders onde Veje og onde Gerninger! Men de hørte ikke og ænsede mig ikke, lyder det fra HERREN.
Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
5 Eders Fædre, hvor er de? Og Profeterne, lever de evigt?
Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
6 Men mine Ord og Bud, som jeg overgav mine Tjenere Profeterne, nåede de ikke eders Fædre, så de måtte vende om og sige: "Som Hærskarers HERRE havde sat sig for at gøre imod os for vore Vejes og Gerningers Skyld, således gjorde han."
Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
7 På den fire og tyvende dag i den ellevte Måned, det er Sjebat Måned, i Darius's andet Regeringsår kom HERRENs Ord til Profeten Zakarias, en Søn af Berekja, en Søn af Iddo, således:
A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
8 Jeg skuede i Nat, og se, en Mand på en rød Hest holdt mellem Bjergene ved den dybe Kløft, og bag ham var der røde, mørke, hvide og brogede Heste.
Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
9 Jeg spurgte: "Hvad betyder de, Herre?" Og Engelen, som talte med mig, sagde: "Jeg vil vise dig, hvad de betyder."
Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
10 Så tog Manden, som holdt mellem Bjergene, til Orde og sagde: "Det er dem, HERREN udsender, for at de skal drage Jorden rundt."
Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
11 Og de tog til Orde og sagde til HERRENs Engel, som stod mellem Bjergene: "Vi drog Jorden rundt, og se, hele Jorden er rolig og stille.
Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
12 HERRENs Engel tog da til Orde og sagde: "Hærskarers HERRE! Hvor længe varer det, før du forbarmer dig over Jerusalem og Judas Byer, som du nu har været vred på i halvfjerdsindstyve År?"
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
13 Og til Svar gav HERREN Engelen, som talte med mig, gode og trøstende Ord.
Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
14 Engelen, som talte med mig, sagde så til mig: Tal og sig: Så siger Hærskarers HERRE: Jeg er fuld af Nidkærhed for Jerusalem og Zion
Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
15 og af Harme mod de trygge Hedninger, fordi de hjalp til at gøre Ulykken stor, da min Vrede kun var lille.
amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
16 Derfor, så siger HERREN: Jeg vender mig til Jerusalem og forbarmer mig over det; mit Hus skal opbygges der, lyder det fra Hærskarers HERRE, og der skal udspændes Målesnor over Jerusalem.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
17 Tal videre: Så siger Hærskarers HERRE: Mine Byer skal atter strømme med Velsignelse, og HERREN vil atter trøste Zion og udvælge Jerusalem.
“Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
18 Derpå løftede jeg mine Øjne og skuede, og se, der var fire Horn.
Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
19 Jeg spurgte Engelen, som talte med mig: "Hvad betyder de?" Han svarede: "Det er de Horn, som har spredt Juda, Israel og Jerusalem."
Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
20 Så lod HERREN mig se fire Smede.
Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
21 Jeg spurgte: "Hvad kommer de for?" Og han svarede: "Hine er de Horn, som spredte Juda, så det ikke kunde løfte sit Hoved; og nu kommer disse for at hvæsse Økser til at slå Hornene til Jorden på de Hedninger, som løftede deres Horn mod Judas Land for at sprede det."
Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”