< Romerne 14 >
1 Men tager eder af den, som er skrøbelig i Troen, og dømmer ikke hans Meninger!
Ku karbi duk wanda yake da rarraunar bangaskiya, ba tare da sukar ra'ayinsa ba.
2 En har Tro til at spise alt; men den skrøbelige spiser kun Urter.
Wani yana da bangaskiyar yaci komai, wani wanda yake da rauni yakanci ganye ne kawai.
3 Den, som spiser, må ikke ringeagte den, som ikke spiser; og den, som ikke spiser, må ikke dømme den, som spiser; thi Gud har taget sig af ham.
Kada wanda yake cin komai ya raina wanda baya cin kowanne abu. Kada kuma wanda baya cin kowanne abu ya shara'anta sauran da suke cin komai. Saboda Allah ya karbe shi.
4 Hvem er du, som dømmer en andens Tjener? For sin egen Herre står eller falder han; men han skal blive stående, thi Herren er mægtig til at lade ham stå.
Kai wanene, kai wanene da kake ganin laifin bawan wani? Tsayawarsa ko faduwarsa ai hakin maigidansa ne, amma Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
5 En agter den ene Dag fremfor den anden, en anden agter alle dage lige; enhver have fuld Vished i sit eget Sind!
Wani yakan daukaka wata rana fiye da sauran. Wani kuma yana daukan ranakun daidai. Kowa ya zauna a cikin hakakkewa akan ra'ayinsa.
6 Den, som lægger Vægt på Dagen, han gør det for Herren. Og den, som spiser, gør det for Herren, thi han takker Gud; og den, som ikke spiser, gør det for Herren og takker Gud.
Shi wanda ya kula da wata rana, ya kula da ita don Ubangiji. Kuma wanda yaci, yaci ne domin Ubangiji, domin yana yi wa Allah godiya. Shi wanda bai ci ba, yaki ci ne domin Ubangiji. Shima yana yi wa Allah godiya.
7 Thi ingen af os lever for sig selv, og ingen dør for sig selv;
Domin babu wanda yake rayuwa don kansa a cikinmu, kuma babu mai mutuwa don kansa.
8 thi når vi leve, leve vi for Herren, og når vi dø, dø vi for Herren; derfor, enten vi leve, eller vi dø, ere vi Herrens.
Domin in muna raye, muna raye don Ubangiji. Kuma in mun mutu, mun mutu ne don Ubangiji. Ashe, ko muna raye, ko a mace mu na Ubangiji ne.
9 Dertil er jo Kristus død og bleven levende, at han skal herske både over døde og levende.
Domin wannan dalilin Almasihu ya mutu ya kuma tashi, saboda ya zama Ubangiji ga matattu da rayayyu.
10 Men du, hvorfor dømmer du din Broder? eller du, hvorfor ringeagter du din Broder? Vi skulle jo alle fremstilles for Guds Domstol.
Amma ku don me kuke shara'anta yan'uwanku? kai kuma don me kake raina dan'uwanka? Dukan mu zamu tsaya gaban kursiyin shari'ar Allah.
11 Thi der er skrevet: "Så sandt jeg lever, siger Herren, for mig skal hvert Knæ bøje sig, og hver Tunge skal bekende Gud."
Domin a rubuce yake, “Na rantse, “inji Ubangiji”, kowacce gwiwa zata rusuna mani, kowanne harshe kuwa zai yabi Allah.”
12 Altså skal hver af os gøre Gud Regnskab for sig selv.
Domin kowannenmu zai fadi abin da shi yayi da bakinsa a gaban Allah.
13 Derfor, lader os ikke mere dømme hverandre, men dømmer hellere dette, at man ikke må give sin Broder Anstød eller Forargelse.
Saboda da haka kada muyi wa juna shari'a, amma maimakon haka ku dauki wannan kudduri, don kada kowa ya zama sanadin tuntunbe ko faduwa ga dan'uwansa.
14 Jeg ved og er vis på i den Herre Jesus, at intet er urent i sig selv; dog, for den, som agter noget for urent, for ham er det urent.
Na sani na kuma tabbata tsakani na da Ubangiji Yesu, ba abin da yake mara tsarki ga asalinsa. Sai dai ga wanda ya dauke shi marar tsarki ne yake zama marar tsarki.
15 Thi dersom din Broder bedrøves for Mads Skyld, da vandrer du ikke mere i Kærlighed. Led ikke ved din Mad den i Fordærvelse, for hvis Skyld Kristus er død.
Idan har abincinka na cutar da dan'uwanka, ba ka tafiya cikin kauna. Kada ka lalata wanda Yesu ya mutu domin sa da abincinka.
16 Lader derfor ikke eders Gode blive bespottet!
Saboda haka, kada abubuwan da aka dauka kyawawa su zama abin zargi ga wadansu.
17 Thi Guds Rige består ikke i at spise og drikke, men i Retfærdighed og Fred og Glæde i den Helligånd.
Saboda mulkin Allah ba maganar ci da sha ba ne, amma game da adalci ne, salama, da farin ciki a cikin Ruhu Mai Tsarki.
18 Thi den, som deri tjener Kristus, er velbehagelig for Gud og tækkelig for Menneskene.
Domin wanda yake bautar Almasihu a wannan hanya, karbabbe ne ga Allah, kuma jama'a sun yarda da shi.
19 Derfor, lader os tragte efter det, som tjener til Fred og indbyrdes Opbyggelse!
Don haka, mu nemi abubuwa na salama da abubuwan da zasu gina juna.
20 Nedbryd ikke Guds Værk for Mads Skyld! Vel er alt rent, men det er ondt for det Menneske, som spiser med Anstød.
Kada ku lalata aikin Allah don abinci. Komai yana da tsarki, amma kaiton mutumin da yake cin abin da zai sa shi ya fadi.
21 Det er rigtigt ikke at spise Kød eller at drikke Vin eller at gøre noget, hvoraf din Broder tager Anstød.
Bashi da kyau a ci nama ko a sha ruwan inabi, ko duk abin da zai jawo faduwar dan'uwanka.
22 Den Tro, du har, hav den hos dig selv for Gud! Salig er den, som ikke dømmer sig selv i det, som han vælger.
Wannan bangaskiyar da kuke da ita, ku adana ta tsakaninku da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa bata da laifi akan abin da hankalinsa ya ga daidai ne.
23 Men den, som tvivler, når han spiser, han er domfældt, fordi det ikke er at Tro; men alt det, som ikke er af Tro, er Synd.
Duk wanda yayi shakka amma kuma yaci, ya sani yayi laifi kenan, domin ba tare da bangaskiya bane. Duk abin da ba na bangaskya bane zunubi ne.