< Aabenbaringen 17 >

1 Og en af de syv Engle, som havde de syv Skåle, kom og talte med mig og sagde: Kom! jeg vil vise dig Dommen over den store Skøge, som sidder over mange Vande,
Daya daga cikin mala'ikun nan bakwai wanda ke rike da tasoshi bakwai ya zo ya ce mani, “Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwarnan da ke zaune a kan ruwaye masu yawa.
2 med hvem Jordens Konger have bolet, og de, som bo på Jorden, ere blevne drukne af hendes Utugts Vin.
Da ita ce sarakunan duniya suka yi fasikanci. Da ruwan inabinta na fasikanci marar dacewa ta sa mazaunan duniya suka bugu.”
3 Og han førte mig i Ånden ud i en Ørken; og jeg så en Kvinde siddende på et skarlagenfarvet Dyr, som var fuldt af Bespottelsens Navne; det havde syv Hoveder og ti Hor1m.
Sai mala'ikan ya dauke ni cikin Ruhu ya tafi da ni jeji, sai na ga mace zaune bisa jan dabba cike da sunayen sabo. Dabbar tana da kawuna bakwai da kahonni goma.
4 Og Kvinden var klædt i Purpur og Skarlagen og strålede af Guld og Ædelsten og Perler; hun havde et Guldbæger i sin Hånd, fuldt af Vederstyggeligheder og hendes Utugts Urenheder.
Matar kuwa tana sanye da tufafi na shunayya da kuma jar garura, ta kuma ci ado da kayan zinariya da duwatsu masu tamani da lu'u-lu'ai. Tana rike da kokon zinariya a hannunta cike da abubuwan kyama da na kazantar fasikancinta marar dacewa.
5 Og på hendes Pande var skrevet et Navn, en Hemmelighed: Babylon den store, Moderen til Jordens Skøger og Vederstyggeligheder.
Bisa goshinta an rubuta wani suna mai boyayyar ma'ana: “Babila mai girma, uwar karuwai da na kazamtattun abubuwan duniya.”
6 Og jeg så Kvinden, drukken af de helliges Blod og af Jesu Vidners Blod; og jeg undrede mig i stor Forundring, da jeg så hende.
Sai na ga matar a buge da jinin masu ba da gaskiya da kuma jinin wadanda aka kashe su domin Yesu. Da na gan ta, na yi mamaki kwarai da gaske.
7 Og Engelen sagde til mig: Hvorfor undrede du dig? Jeg vil sige dig Hemmeligheden med Kvinden og med Dyret, som bærer hende, og som har de syv Hoveder og de ti Horn.
Amma mala'ikan ya ce mani, “Don me kake mamaki? Zan bayyana maka ma'anar matar da kuma na dabbar da ke dauke da ita, dabban nan da ke da kawuna bakwai da kahonni goma.
8 Dyret, som du så, har været og er ikke, og det skal stige op af Afgrunden og gå bort til Fortabelse; og de, som bo på Jorden, skulle undre sig, de, hvis Navne ikke ere skrevne i Livets Bog fra Verdens Grundlæggelse, når de se, at Dyret var og er ikke og skal komme. (Abyssos g12)
Dabban da ka gani da, yanzu ba ta, amma ta na kusan hawowa daga rami marar iyaka. Sa'annan za ta je hallaka. Wadanda ke zaune a duniya, wadanda ba a rubuta sunayensu cikin littafin rai ba tun kafuwar duniya - za su yi mamaki idan suka ga dabbar da da ta kasance, ba ta nan yanzu, amma ta kusa zuwa. (Abyssos g12)
9 Her gælder det den Forstand, som har Visdom. De syv Hoveder ere syv Bjerge, på hvilke Kvinden sidder,
Wannan al'amari na bukatar hikima. Kawunnan bakwai, tuddai ne bakwai da macen ke zaune a kai.
10 og de ere syv Konger. De fem ere faldne, den ene er der, den anden er endnu ikke kommen, og når han kommer, skal han blive en liden Tid.
Su kuma sarakuna ne bakwai. Sarakuna biyar sun fadi, daya na nan, amma dayan bai zo ba tukuna; sa'anda ya zo zai kasance na dan lokaci kadan.
11 Og Dyret, som var og er ikke, er både selv en ottende og er en af de syv og farer bort til Fortabelse.
Dabban da ya kasance a da, amma yanzu ba shi, shi ma sarki ne na takwas; amma shi daya ne cikin sarakunan nan bakwai, kuma zai tafi hallaka.
12 Og de ti Horn, som du så, ere ti Konger, som endnu ikke have fået Rige, men få Magt som Konger een Time sammen med Dyret.
Kahonnin nan goma da ka gani sarakuna goma ne wadanda ba a nada su ba tukuna, amma za su karbi iko kamar na sarakai na sa'a daya tare da dabban.
13 Disse have eet Sind, og deres Kraft og Magt give de til Dyret.
Ra'ayinsu daya ne, za su ba da sarautarsu da ikon su ga dabban.
14 Disse skulle føre Krig med Lammet, og Lammet skal sejre over dem - fordi det er Herrers Herre og Kongers Konge - og de: som ere med det, de kaldede og udvalgte og trofaste.
Za su yi yaki da Dan Rago. Dan Ragon zai ci nasara a kansu domin shi Ubangijin iyayengiji ne da Sarkin sarakuna - kuma tare da shi sune kirayayyun, zababbun, amintattun.”
15 Og han sagde til mig: De Vande, som du så, der hvor Skøgen sidder, ere Folk og Skarer og Folkeslag og Tungemål.
Mala'ikan ya ce mani, “Ruwayen da ka gani, inda karuwar ke zaune, jama'a ce, da taro masu dumbin yawa, da al'ummai da harsuna.
16 Og de ti Horn, som du så, og Dyret, disse ville hade Skøgen og gøre hende øde og nøgen og æde hendes Kød og opbrænde hende med Ild.
Kahonnin nan goma da ka gani - su da dabban za su ki karuwar. Za su washe ta su tsiranceta, za su lankwame namanta, za su kone ta gaba daya da wuta.
17 Thi Gud har indgivet dem i deres Hjerte at gøre efter hans Sind og at handle af eet Sind og at give Dyret deres Kongemagt, indtil Guds Ord blive fuldbyrdede.
Gama Allah ya sa a zukantansu su yi nufinsa ta wurin amincewarsa, su sadaukar da ikonsu na yin mulki ga dabban har sai maganar Allah ta cika.
18 Og Kvinden, som du så, er den store Stad, som har Herredømme over Jordens Konger.
Matar da ka gani ita ce babban birnin nan da ke mulki bisa sarakunan duniya.”

< Aabenbaringen 17 >