< Aabenbaringen 16 >

1 Og jeg hørte en høj Røst fra Tempelet sige til de syv Engle: Går hen og udgyder Guds Harmes syv Skåle over Jorden!
Sai na ji wata babbar murya daga haikalin tana ce wa mala’iku bakwai nan, “Ku tafi ku zuba kwanoni bakwai nan na fushin Allah a kan duniya.”
2 Og den første gik hen og udgød sin Skål over Jorden, og der kom slemme og onde Bylder på de Mennesker, som havde Dyrets Mærke, og dem, som tilbade dets Billede.
Mala’ika na fari ya je ya juye kwanonsa a bisan ƙasa, sai munanan gyambuna masu zafi suka fito a jikin mutanen da suke da alamar dabbar suka kuma yi wa siffarta sujada.
3 Og den anden Engel udgød sin Skål i Havet, og det blev til Blod som af en død; og hver levende Sjæl i Havet døde.
Mala’ika na biyu ya juye kwanonsa a bisan teku, sai tekun ya zama jini kamar na mataccen mutum, kuma kowane abu mai rai da yake cikin tekun ya mutu.
4 Og den tredje Engel udgød sin Skål i Floderne og Vandkilderne, og de bleve til Blod.
Mala’ika na uku ya juye kwanonsa a bisan koguna da maɓulɓulan ruwa, sai suka zama jini.
5 Og jeg hørte Vandenes Engel sige: Retfærdig er du, som er, og som var, du hellige, fordi du har fældet denne Dom;
Sa’an nan na ji mala’ikan da yake lura da ruwaye ya ce, “Kai mai adalci ne cikin waɗannan hukuntai, kai da kake yanzu, kake kuma a dā, Mai Tsarki, saboda yadda ka yi hukuncin nan;
6 thi de have udøst helliges og Profeters Blod, og du har givet dem Blod at drikke; de ere det værd.
gama sun zub da jinin tsarkakanka da kuma annabawanka, ka kuwa ba su jini su sha, yadda ya dace da su.”
7 Og jeg hørte Alteret sige: Ja, Herre, Gud, du almægtige! sande og retfærdige ere dine Domme.
Na kuma ji bagaden ya amsa, “I, Ubangiji Allah, Maɗaukaki, hukuntanka daidai yake na adalci ne kuma.”
8 Og den fjerde Engel udgød sin Skål over Solen; og det blev givet den at brænde Menneskene med Ild.
Mala’ika na huɗu ya juye kwanonsa a bisan rana, sai aka ba wa rana iko ta ƙona mutane da wuta.
9 Og Menneskene brændtes i stor Hede og bespottede Guds Navn, som har Magt over disse Plager; og de omvendte sig ikke til at give ham Ære.
Aka ƙone su da zafin wuta mai tsanani suka kuwa la’anci sunan Allah wanda yake da iko a kan waɗannan annoban, amma suka ƙi su tuba su kuma ɗaukaka shi.
10 Og den femte Engel udgød sin Skål over Dyrets Trone; og dets Rige blev formørket, og de tyggede deres Tunger af Pine.
Mala’ika na biyar ya juye kwanonsa a bisan gadon sarautar dabbar, mulkinta kuwa ya zama duhu. Mutane suka yi ta cizon bakinsu saboda azaba
11 Og de bespottede Himmelens Gud for deres Piner og for deres Bylder; og de omvendte sig ikke fra deres Gerninger.
suka kuma la’anci Allah na sama saboda zafinsu, da kuma saboda gyambunansu, amma suka ƙi su tuba daga abin da suka riga suka yi.
12 Og den sjette Engel udgød sin Skål over den store Flod Eufrat; og dens Vand borttørredes, for at Vejen kunde beredes for Kongerne fra Solens Opgang.
Mala’ika na shida ya juye kwanonsa a bisan babban kogin Yuferites, sai ruwansa ya shanye don a shirya hanya saboda sarakuna daga Gabas.
13 Og jeg så, at der af Dragens Mund og af Dyrets Mund og af den falske Profets Mund udgik tre urene Ånder, som lignede Padder.
Sa’an nan na ga mugayen ruhohi guda uku da suka yi kamar kwaɗi; suka fito daga bakin macijin nan, da kuma daga bakin dabbar, da kuma daga bakin annabin ƙaryan nan.
14 Thi de ere DæmonersÅnder, som gøre Tegn; og de gå ud til hele Jorderiges Konger for at samle dem til Krigen på Guds, den almægtiges, store Dag.
Su ruhohin aljanu ne da suke aikata abubuwan banmamaki, sukan je wurin sarakunan dukan duniya, don su tattara su don yaƙi a babbar ranar Allah Maɗaukaki.
15 - Se, jeg kommer som en Tyv Salig er den, som våger og bevarer sine Klæder, så han ikke skal gå nøgen, og man skal se hans Skam. -
“Ga shi, ina zuwa kamar ɓarawo! Mai albarka ne wanda yake zama a faɗake yana kuma saye da tufafinsa, don kada yă yi tafiya tsirara a kuma kunyata shi.”
16 Og de samlede dem til det Sted, som kaldes på Hebraisk Harmagedon.
Sa’an nan aka tattara sarakuna zuwa wurin da a Ibraniyanci ake kira Armageddon.
17 Og den syvende Engel udgød sin Skål i Luften; og fra Templet, fra Tronen udgik der en høj Røst, som sagde: Det er sket.
Mala’ika na bakwai ya juye kwanonsa cikin iska, daga haikalin kuwa sai aka ji wata babbar murya daga kursiyin, tana cewa, “An gama!”
18 Og der kom Lyn og Røster og Tordener; og der blev et stort Jordskælv, hvis Mage ikke har været, siden der blev Mennesker til på Jorden, et sådant Jordskælv, så stort.
Sai ga walƙiya, ƙararraki, tsawa da kuma matsananciyar girgizar ƙasa. Ba a taɓa yin irin wannan girgizar ƙasar ba, tun kasancewar mutum a duniya, girgizar ƙasar kuwa gawurtacciya ce.
19 Og den store Stad blev til tre Dele, og Folkeslagenes Stæder faldt; og Gud kom det store Babylon i Hu for at give det Bægeret med sin Vredes Harmes Vin.
Babban birnin ya rabu kashi uku, biranen al’ummai kuma suka rurrushe. Allah ya tuna da Babilon Mai Girma ya kuma ba ta kwaf cike da ruwan inabin fushinsa.
20 Og hver Ø flyede, og Bjerge bleve ikke fundne.
Kowane tsibiri ya gudu ba a kuwa ƙara ganin duwatsu ba.
21 Og en stærk Hagl, centnertung, faldt ned fra Himmelen på Menneskene; og Menneskene bespottede Gud for Haglens Plage, thi dens Plage var meget stor.
Daga sararin sama manyan ƙanƙara masu nauyin gaske suka fāɗo a kan mutane. Suka kuma la’anci Allah saboda annobar ƙanƙarar, domin annobar ta yi muni ƙwarai.

< Aabenbaringen 16 >