< Salme 89 >

1 (En Maskil af Ezraitten Etan.) Om HERRENs, Nåde vil jeg evigt synge, fra Slægt til Slægt med min Mund forkynde din Trofasthed.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Thi du har sagt: "En evig Bygning er Nåden!" I Himlen har du grundfæstet din Trofasthed.
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 Jeg sluttede en Pagt med min udvalgte, tilsvor David, min Tjener:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 "Jeg lader din Sæd bestå for evigt, jeg bygger din Trone fra Slægt til Slægt!" (Sela)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 Og Himlen priser dit Under, HERRE, din Trofasthed i de Helliges Forsamling.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Thi hvem i Sky er HERRENs Lige, hvo er som HERREN iblandt Guds Sønner?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 En forfærdelig Gud i de Helliges Kreds, stor og frygtelig over alle omkring ham.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 HERRE, Hærskarers Gud, hvo er som du? HERRE, din Nåde og Trofasthed omgiver dig.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Du mestrer Havets Overmod; når Bølgerne bruser, stiller du dem.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Du knuste Rahab som en fældet Kriger, splitted dine Fjender med vældig Arm.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 Din er Himlen, og din er Jorden, du grundede Jorderig med dets Fylde.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Norden og Sønden skabte du, Tabor og Hermon jubler over dit Navn.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Du har en Arm med Vælde, din Hånd er stærk, din højre løftet.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 Retfærd og Ret er din Trones Grundvold, Nåde og Sandhed står for dit Åsyn.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Saligt det Folk, der kender til Frydesang, vandrer, HERRE, i dit Åsyns Lys!
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 De lovsynger Dagen igennem dit Navn, ophøjes ved din Retfærdighed.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Thi du er vor Styrkes Stolthed, du løfter vort Horn ved din Yndest;
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 thi vort Skjold er hos HERREN, vor Konge er Israels Hellige!
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Du taled engang i et Syn til dine fromme: "Krone satte jeg på en Helt, ophøjed en Yngling af Folket;
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 jeg har fundet David, min Tjener, salvet ham med min hellige Olie;
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 thi min Hånd skal holde ham fast, og min Arm skal give ham Styrke.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 Ingen Fjende skal overvælde ham, ingen Nidding trykke ham ned;
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 jeg knuser hans Fjender foran ham og nedstøder dem, der bader ham;
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 med ham skal min Trofasthed og Miskundhed være, hans Horn skal løfte sig ved mit Navn;
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 jeg lægger Havet under hans Hånd og Strømmene under hans højre;
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 mig skal han kalde: min Fader, min Gud og min Frelses Klippe.
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Jeg gør ham til førstefødt, den største blandt Jordens Konger;
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 jeg bevarer for evigt min Miskundhed mod ham, min Pagt skal holdes ham troligt;
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 jeg lader hans Æt bestå for evigt, hans Trone, så længe Himlen er til.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Hvis hans Sønner svigter min Lov og ikke følger mine Lovbud,
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 hvis de bryder min Vedtægt og ikke holder mit Bud,
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 da hjemsøger jeg deres Synd med Ris, deres Brøde med hårde Slag;
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 men min Nåde tager jeg ikke fra ham, min Trofasthed svigter jeg ikke;
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 jeg bryder ikke min Pagt og ændrer ej mine Læbers Udsagn.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 Ved min Hellighed svor jeg een Gang for alle - David sviger jeg ikke:
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 Hans Æt skal blive for evigt, hans Trone for mig som Solen,
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 stå fast som Månen for evigt, og Vidnet på Himlen er sanddru, (Sela)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Men du har forstødt og forkastet din Salvede og handlet i Vrede imod ham;
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Pagten med din Tjener har du brudt, vanæret hans Krone og trådt den i Støvet;
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 du har nedbrudt alle hans Mure, i Grus har du lagt hans Fæstninger;
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 alle vejfarende plyndrer ham, sine Naboer blev han til Spot.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Du har løftet hans Uvenners højre og glædet alle hans Fjender;
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 hans Sværd lod du vige for Fjenden, du holdt ham ej oppe i Kampen;
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 du vristed ham Staven af Hænde og styrted hans Trone til Jorden,
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 afkorted hans Ungdoms Dage og hylled ham ind i Skam. (Sela)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Hvor længe vil du skjule dig, HERRE, for evigt, hvor længe skal din Vrede lue som Ild?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Herre, kom i Hu, hvad Livet er, til hvilken Tomhed du skabte hvert Menneskebarn!
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Hvo bliver i Live og skuer ej Død, hvo frelser sin sjæl fra Dødsrigets Hånd? (Sela) (Sheol h7585)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
49 Hvor er din fordums Nåde, Herre, som du i Trofasthed tilsvor David?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Kom, Herre, din Tjeners Skændsel i Hu, at jeg bærer Folkenes Spot i min Favn,
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 hvorledes dine Fjender håner, HERRE, hvorledes de håner din Salvedes Fodspor.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Lovet være HERREN i Evighed, Amen, Amen!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!

< Salme 89 >