< Salme 77 >

1 (Til Sangmesteren. Til Jedutun. Af Asaf. En Salme.) Jeg råber, højt til Gud, og han hører mig,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 jeg søger Herren på Nødens Dag, min Hånd er om Natten utrættet udrakt, min Sjæl vil ikke lade sig trøste;
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 jeg ihukommer Gud og stønner, jeg sukker, min Ånd vansmægter. (Sela)
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 Du holder mine Øjne vågne, jeg er urolig og målløs.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 Jeg tænker på fordums dage, ihukommer længst henrundne År;
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 jeg gransker om Natten i Hjertet, grunder og ransager min Ånd.
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 Vil Herren bortstøde for evigt og aldrig mer vise Nåde,
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 er hans Miskundhed ude for stedse, hans Trofasthed omme for evigt og altid,
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 har Gud da glemt at ynkes, lukket sit Hjerte i Vrede? (Sela)
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 Jeg sagde: Det er min Smerte; at den Højestes højre er ikke som før.
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 Jeg kommer HERRENs Gerninger i Hu, ja kommer dine fordums Undere i Hu.
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 Jeg tænker på al din Gerning og grunder over dine Værker.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 Gud, din Vej var i Hellighed, hvo er en Gud så stor som Gud!
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 Du er en Gud, som gør Undere, du gjorde din Vælde kendt blandt Folkene,
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 udøste dit Folk med din Arm, Jakobs og Josefs Sønner. (Sela)
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 Vandene så dig, Gud, Vandene så dig og vred sig i Angst, ja Dybet tog til at skælve;
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 Skyerne udøste Vand, Skyhimlens Stemme gjaldede, dine Pile for hid og did;
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 din bragende Torden rullede, Lynene oplyste Jorderig, Jorden bæved og skjalv;
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 din Vej gik midt gennem Havet, din Sti gennem store Vande, dine Fodspor kendtes ikke.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 Du førte dit Folk som en Hjord ved Moses's og Arons Hånd.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.

< Salme 77 >