< Salme 75 >
1 (Til Sangmesteren. Al-tasjhet. En Salme af Asaf. En sang.) Vi takker dig, Gud, vi takker dig; de, der påkalder dit Navn, fortæller dine Undere.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
2 "Selv om jeg udsætter Sagen, dømmer jeg dog med Retfærd;
Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
3 vakler end Jorden og alle, som bor derpå, har jeg dog grundfæstet dens Støtter." (Sela)
Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
4 Til Dårerne siger jeg: "Vær ej Dårer!" og til de gudløse: "Løft ej Hornet,
Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
5 løft ikke eders Horn mod Himlen, tal ikke med knejsende Nakke!"
Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
6 Thi hverken fra Øst eller Vest kommer Hjælp, ej heller fra Ørk eller Bjerge.
Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
7 Nej, den, som dømmer, er Gud, han nedbøjer en, ophøjer en anden.
Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
8 Thi i HERRENs Hånd er et Bæger med skummende, krydet Vin. han skænker i for een efter een, selv Bærmen drikker de ud; alle Jordens gudløse drikker.
A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
9 Men jeg skal juble evindelig, lovsynge Jakobs Gud;
Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
10 alle de gudløses Horn stødes af, de retfærdiges Horn skal knejse!
wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”