< Salme 74 >
1 (En maskil af Asaf.) Hvorfor har du, Gud, stødt os bort for evig, hvi ryger din Vrede mod Hjorden, du røgter?
Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
2 Kom din Menighed i Hu, som du fordum vandt dig, - du udløste den til din Ejendoms Stamme - Zions Bjerg, hvor du har din Bolig.
Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
3 Løft dine Fjed til de evige Tomter: Fjenden lagde alt i Helligdommen øde.
Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
4 Dine Fjender brøled i dit Samlingshus, satte deres Tegn som Tegn deri.
Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
5 Det så ud, som når man løfter Økser i Skovens Tykning.
Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
6 Og alt det udskårne Træværk der! De hugged det sønder med Økse og Hammer.
Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
7 På din Helligdom satte de Ild, de skændede og nedrev dit Navns Bolig.
Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
8 De tænkte: "Til Hobe udrydder vi dem!" De brændte alle Guds Samlingshuse i Landet.
Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
9 Vore Tegn, dem ser vi ikke, Profeter findes ej mer; hvor længe, ved ingen af os.
Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
10 Hvor længe, o Gud, skal vor Modstander smæde, Fjenden blive ved at håne dit Navn?
Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
11 Hvorfor holder du din Hånd tilbage og skjuler din højre i Kappens Fold?
Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
12 Vor Konge fra fordums Tid er dog Gud, som udførte Frelsens Værk i Landet.
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
13 Du kløvede Havet med Vælde, knuste på Vandet Dragernes Hoved;
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
14 du søndrede Hovederne på Livjatan og gav dem som Æde til Ørkenens Dyr;
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
15 Kilde og Bæk lod du vælde frem, du udtørred stedseflydende Strømme;
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
16 din er Dagen, og din er Natten, du grundlagde Lys og Sol,
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
17 du fastsatte alle Grænser på Jord, du frembragte Sommer og Vinter.
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
18 Kom i Hu, o HERRE, at Fjenden har hånet, et Folk af Dårer har spottet dit Navn!
Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
19 Giv ikke Vilddyret din Turteldues Sjæl, glem ikke for evigt dine armes Liv;
Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
20 se hen til Pagten, thi fyldte er Landets mørke Steder med Voldsfærds Boliger.
Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
21 Lad ej den fortrykte gå bort med Skam, lad de arme og fattige prise dit Navn!
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
22 Gud, gør dig rede, før din Sag, kom i Hu, hvor du stadig smædes af bårer,
Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
23 lad ej dine Avindsmænds Røst uænset! Ustandseligt lyder dine Fjenders Larm!
Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.