< Salme 71 >
1 HERRE, jeg lider på dig, lad mig aldrig i evighed skuffes.
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2 Frels mig og udfri mig i din Retfærdighed, du bøjede dit Øre til mig;
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3 red mig og vær mig en Tilflugtsklippe, en Klippeborg til min Frelse; thi du er min Klippe og Borg!
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
4 Min Gud, fri mig ud af gudløses Hånd, af Niddings og Voldsmands Kløer;
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
5 thi du er mit Håb, o Herre! Fra min Ungdom var HERREN min Tillid;
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
6 fra Moders Skød har jeg støttet mig til dig, min Forsørger var du fra Moders Liv, dig gælder altid min Lovsang.
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
7 For mange står jeg som mærket af Gud, men du er min stærke Tilflugt;
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
8 min Mund er fuld af din Lovsang, af din Ære Dagen lang.
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
9 Forkast mig ikke i Alderdommens Tid og svigt mig ikke, nu Kraften svinder;
Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
10 thi mine Fjender taler om mig, de der lurer på min Sjæl, holder Råd:
Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
11 "Gud har svigtet ham! Efter ham! Grib ham, thi ingen frelser!"
Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
12 Gud, hold dig ikke borte fra mig, il mig til Hjælp, min Gud;
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
13 lad dem blive til Skam og Skændsel, dem, der står mig imod, lad dem hylles i Spot og Spe, dem, der vil mig ondt!
Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
14 Men jeg, jeg vil altid håbe, blive ved at istemme din Pris;
Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
15 min Mund skal vidne om din Retfærd, om din Frelse Dagen lang; thi jeg kender ej Ende derpå.
Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
16 Jeg vil minde om den Herre HERRENs Vælde, lovsynge din Retfærd, kun den alene.
Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
17 Gud, du har vejledt mig fra min Ungdom af, dine Undere har jeg forkyndt til nu;
Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
18 indtil Alderdommens Tid og de grånende Hår svigte du mig ikke, o Gud. End skal jeg prise din Arm for alle kommende Slægter.
Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
19 Din Vælde og din Retfærdighed når til Himlen, o Gud; du, som øvede store Ting, hvo er din Lige, Gud?
Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
20 Du, som lod os skue mange fold Trængsel og Nød, du kalder os atter til Live og drager os atter af Jordens Dyb;
Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
21 du vil øge min Storhed og atter trøste mig.
Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
22 Til Gengæld vil jeg til Harpespil prise din Trofasthed, min Gud, lege på Citer for dig, du Israels Hellige;
Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
23 juble skal mine Læber - ja, jeg vil lovsynge dig og min Sjæl, som du udløste;
Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
24 også min Tunge skal Dagen igennem forkynde din Retfærd, thi Skam og Skændsel får de, som vil mig ilde.
Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.