< Salme 6 >
1 (Til sangmesteren. Med strengespil. Efter den ottende. En salme af David.) HERRE, revs mig ej i din Vrede, tugt mig ej i din Harme,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 vær mig nådig Herre, jeg sygner hen, mine Ledmod skælver, læg mig, Herre!
Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
3 Såre skælver min Sjæl; o HERRE, hvor længe endnu?
Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
4 Vend tilbage, HERRE, og frels min Sjæl, hjælp mig dog for din Miskundheds Skyld!
Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
5 Thi i Døden kommes du ikke i Hu, i Dødsriget hvo vil takke dig der? (Sheol )
Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol )
6 Jeg er så træt af at sukke; jeg væder hver Nat mit Leje, bader med Tårer min Seng;
Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
7 mit Øje hentæres af Sorg, sløves for alle mine Fjenders Skyld.
Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
8 Vig fra mig, alle I Udådsmænd, thi HERREN har hørt min Gråd,
Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
9 HERREN har hørt min Tryglen, min Bøn tager HERREN imod.
Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
10 Beskæmmes skal alle mine Fjender og såre forfærdes, brat skal de vige med Skam.
Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.