< Salme 55 >

1 (Til sangmesteren. Med strengespil. En maskil af David.) Lyt, o Gud, til min Bøn, skjul dig ej for min tryglen,
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 lå mig Øre og svar mig, jeg vånder mig i Klage,
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 jeg stønner ved Fjendernes Råb og de gudløses Skrig; thi Ulykke vælter de over mig, forfølger mig grumt;
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 Hjertet er angst i mit Bryst, Dødens Rædsler er faldet over mig.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 Frygt og Angst falder på mig, Gru er over mig.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 Jeg siger: Ak, havde jeg Vinger som Duen, da fløj jeg i Ly,
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 ja, langt bort vilde jeg fly og blive i Ørkenen. (Sela)
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 Da søgte jeg skyndsomt Tilflugt for rivende Storm og Uvejr.
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Herre, forvir og split deres Tungemål! Thi Vold og Ufred ser jeg i Byen;
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 de går Rundgang Dag og Nat på dens Mure;
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 Ulykke, Kvide og Vanheld råder derinde, Voldsfærd og Svig viger aldrig bort fra dens Torve.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 Det var ikke en Fjende, som hånede mig - det kunde bæres; min uven ydmygede mig ej - ham kunde jeg undgå;
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 men du, en Mand af min Stand, en Ven og fortrolig,
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 og det skønt vi delte Samværets Sødme, vandrede endrægtelig i Guds Hus.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Over dem komme Død, lad dem levende synke i Dødsriget! Thi der er Ondskab i deres Bolig, i deres Indre! (Sheol h7585)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
16 Jeg, jeg råber til Gud, og HERREN vil frelse mig.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 Jeg klager og stønner ved Kvæld, ved Gry og ved Middag; min Røst vil han høre
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 og udfri min Sjæl i Fred, så de ikke kan komme mig nær; thi mange er de imod mig.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 Gud, som troner fra Fortids Dage, vil høre og ydmyge dem. (Sela) Thi der er ingen Forandring hos dem, og de frygter ikke for Gud.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 På Venner lagde han Hånd og brød sin Pagt.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 Glattere end Smør er hans Mund, men Hjertet vil Krig, blødere end Olie hans Ord, skønt dragne Sværd.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Kast din Byrde på HERREN, så sørger han for dig, den retfærdige lader han ikke i Evighed rokkes.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 Og du, o Gud, nedstyrt dem i Gravens Dyb! Ej skal blodstænkte, svigefulde Mænd nå Hælvten af deres Dage. Men jeg, jeg stoler på dig!
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< Salme 55 >